ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 

by Ibrahim Bala
3 months ago

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, wanda muke zaƙulo batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.

A wannan gaɓar zan ja hankalin matasa da kuma iyaye musamman maza. An shiga wani yanayi da sai dai mu yi addu’a, mu riƙa ƙoƙari muna daina amfani da kalmar taluaci muna yin ɓarna, wannan ba daidai ba ne.

Babu yadda za a yi talauci ya saka saɓon Allah, wannan ba daidai ba ne ba. Dole ne mu ja hankali mu kiyaye, samari ne lungu da saƙo gasu nan an koya musu sana’ar sayar da kayan maye, wannan kuma sai dai mu ce innalillahi wa inna ilaihirraji’un.

ADVERTISEMENT
  • Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
  • Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

A gefe guda ɓarna tana ta wanzuwa har da matan aure ake kai wa ajiyar ƙwayoyi, idan an je siya sai a riƙa shiga gidajen ana karɓa ana siya, kuma ana fakewa da cewa wai talauci ne yake janyo wa, wannan ba daidai ba ne ba.

Allah ya baka rai, ya baka lafiya, to, ya baka damar da za ka tsaya ka nemi abin da za ka dafa ka rufawa kanka asiri. Ka shayar da iyalinka halal ba haram ba. Sannan kai matashi ka tsaya ka nemi halaliyarka.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

Wannan shi ya sa kodayaushe a rayuwa muke shiga cikin wani yanayi, kamar ka haifi ‘ya’ya a rasa yadda za a yi da su, ba dan komai ba saboda neman da aka yi ba a tsaya an yi shi na tsakani ga Allah ba, an bi ta ɓarauniyar hanya wajen tara dukiyar da aka mallaki iyalan.

Ina ganin ya kamata mu tsaya mu yi wa kanmu faɗa halin da ƙasar take ciki, kullum cewa muke yi shugabanni kaza! Shugabanni kaza!! bayan mu, ba ma duba mu me muke yi? to, dole mu zauna idan kai magidanci ne kai ka tsaya ka san ma ‘yaƴanka wacce irin sana’a suke yi da suke samun kuɗi. Saurayin ‘yar ka me yake yi ma, da har yake zuwa gurinta ya siya mata abu kaza?.

Kar idonmu ya rufe mu riƙa ganin wane yana samun kuɗi, sana’a ce wacce take kawo kuɗi. Mu kalli halaliyar, kaɗan me albarka ya fi me yawa mara albarka. Mu tsaya mu mayar da hankali saboda hadisi ne ingantacce cewar, kai hani da aljihunka, ko da hannunka, ko da bakinka.

Indai waɗannan abubuwa da za su kawo tangarɗa ko cutuwa ga al’ummar musulmi to, ya kamata saboda sayar da kwayoyi ya kan iya sakawa samari su aikata abubuwan da ba acikin tunaninsu da hankalinsu suke ba. Lokaci ne da ya kamata mu yarda cewar, daga gidajenmu za mu fara ɗaukar matakin gyara, sannan mu fita waje.

Amma a gidanka ka bar baya da ƙura, baka tsaya ka tsananta ka yi faɗa ga ‘yaƴanka ba, kai dai kawai ana shigo maka da abinci, ‘yaƴanka sukan iya ɗaukar nauyinka na kuɗin makaranta ko suturar da za ka saka sai ka ja baki ka yi shuru.

Dole ne wannan abun mu hankalta da shi, wallahi wannan abun ya fara shiga lunguna da saƙo. Wasu ɓata gari suna zuwa suna rabawa yara kwayoyi suna siyarwa suna samun riba me yawa. Dole ne mu magance wannan matsalar, kafin a ci mu da yaƙi.

Wassalamu Alaikum.

Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Next Post
Hukumar Shari’a Ta Kano Ta Hukunta Alƙalai Da Ma’aikata Kan Laifukan Rashin Ɗa’a

Hukumar Shari’a Ta Kano Ta Hukunta Alƙalai Da Ma’aikata Kan Laifukan Rashin Ɗa'a

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.