Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu. Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, wanda muke zaƙulo batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.
A wannan gaɓar zan ja hankalin matasa da kuma iyaye musamman maza. An shiga wani yanayi da sai dai mu yi addu’a, mu riƙa ƙoƙari muna daina amfani da kalmar taluaci muna yin ɓarna, wannan ba daidai ba ne.
Babu yadda za a yi talauci ya saka saɓon Allah, wannan ba daidai ba ne ba. Dole ne mu ja hankali mu kiyaye, samari ne lungu da saƙo gasu nan an koya musu sana’ar sayar da kayan maye, wannan kuma sai dai mu ce innalillahi wa inna ilaihirraji’un.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
A gefe guda ɓarna tana ta wanzuwa har da matan aure ake kai wa ajiyar ƙwayoyi, idan an je siya sai a riƙa shiga gidajen ana karɓa ana siya, kuma ana fakewa da cewa wai talauci ne yake janyo wa, wannan ba daidai ba ne ba.
Allah ya baka rai, ya baka lafiya, to, ya baka damar da za ka tsaya ka nemi abin da za ka dafa ka rufawa kanka asiri. Ka shayar da iyalinka halal ba haram ba. Sannan kai matashi ka tsaya ka nemi halaliyarka.
Wannan shi ya sa kodayaushe a rayuwa muke shiga cikin wani yanayi, kamar ka haifi ‘ya’ya a rasa yadda za a yi da su, ba dan komai ba saboda neman da aka yi ba a tsaya an yi shi na tsakani ga Allah ba, an bi ta ɓarauniyar hanya wajen tara dukiyar da aka mallaki iyalan.
Ina ganin ya kamata mu tsaya mu yi wa kanmu faɗa halin da ƙasar take ciki, kullum cewa muke yi shugabanni kaza! Shugabanni kaza!! bayan mu, ba ma duba mu me muke yi? to, dole mu zauna idan kai magidanci ne kai ka tsaya ka san ma ‘yaƴanka wacce irin sana’a suke yi da suke samun kuɗi. Saurayin ‘yar ka me yake yi ma, da har yake zuwa gurinta ya siya mata abu kaza?.
Kar idonmu ya rufe mu riƙa ganin wane yana samun kuɗi, sana’a ce wacce take kawo kuɗi. Mu kalli halaliyar, kaɗan me albarka ya fi me yawa mara albarka. Mu tsaya mu mayar da hankali saboda hadisi ne ingantacce cewar, kai hani da aljihunka, ko da hannunka, ko da bakinka.
Indai waɗannan abubuwa da za su kawo tangarɗa ko cutuwa ga al’ummar musulmi to, ya kamata saboda sayar da kwayoyi ya kan iya sakawa samari su aikata abubuwan da ba acikin tunaninsu da hankalinsu suke ba. Lokaci ne da ya kamata mu yarda cewar, daga gidajenmu za mu fara ɗaukar matakin gyara, sannan mu fita waje.
Amma a gidanka ka bar baya da ƙura, baka tsaya ka tsananta ka yi faɗa ga ‘yaƴanka ba, kai dai kawai ana shigo maka da abinci, ‘yaƴanka sukan iya ɗaukar nauyinka na kuɗin makaranta ko suturar da za ka saka sai ka ja baki ka yi shuru.
Dole ne wannan abun mu hankalta da shi, wallahi wannan abun ya fara shiga lunguna da saƙo. Wasu ɓata gari suna zuwa suna rabawa yara kwayoyi suna siyarwa suna samun riba me yawa. Dole ne mu magance wannan matsalar, kafin a ci mu da yaƙi.
Wassalamu Alaikum.















Discussion about this post