Tarihin kwalejin Barewa wani babban lamari ne wanda ya sha yawan sauye-sauye ko canje- canje, labarin dai ya fara ne daga Katsina lokacin da aka kafa kwalejin horarwa ta Katsina.
Shawarar lamarin kafa ita kwalejin abin ya faru ne daga bangaren mai rikon mukamin Darekatn ilimi na Lardunan Arewa, Mista. F.M.Urling Smith da aka fi sani da (Malam Smith) wanda shi an san shi yana da bukatar samun karuwar ingantaccen ilimi ta hanyar samar da Malaman makaranta da suka samu horarwar.Tunda akwai bukatar ilimi a Lardunan Arewacin Nijeriya dole abin ya tafi tare da“yan asalin wurin”,don haka ne shi Urling Smith ya fahimci cewar akwai bukatar ingancin Malaman Afirka ko ma’aikata.Kamar yadda Urling Smith ya ke hasashe na ya dace a samu aji domin koyar da Malaman makaranta kamar yadda ya dace.Saboda kuwa ya nuna matukar damuwa akan yadda tsarin ilimin ya ke yi tafiyar Kura,zai kuma ci gaba da,ayi hakan, matukar ba a samu Malamai na nahiyar Afirka ba wadanda za a iya basu horon da ya dace fiye da wadanda ake da su.Manufar ita ce bukatar samar da abubuwan koyarwa na kafa ta musamman ta koyarwa, da za ta taimakawa sauran Jami’an mulkin mallaka kamar su, Hans Bischer (Dan Hausa) wanda yake shi Darektan ilimi ne tun farko ne ya ki bada goyon baya na wata makaranta a tsakiya da za a ce ta fi samun ci gaba fiye da sauran.Duk da yake dai,Lord Frederick Lugard Gwamna mai kare ko kula da Arewacin Nijeriya ya sa al’amarin a cikin abubuwan da, ya ke son yi a shekarar 1917, sai dai kash! aka ki aminewa da shawarar ta shi saboda rashin Kudi da kuma da kuma ma’aikata.
Lamarin bai samu wani tagomashi ba sai zuwan wani sabon Gwamna,da ake kira Sir Hugh Clifford a lokacin shi ne maganar ta samu amincewa. Babbar manufar abin ita ce ilimi a Lardunan Arewa ba wai ana bukatar a horar da ‘yan Arewar ba ne domin su yi gogaiya da sauran ‘yan Afirka ba ne wajen neman ayyukan gwamnati ba,maimakon hakan shi sashen ilimi zai kasance wani abu ne da za ayi amfani da shi wajen yin aiki wajen tafiyar da ayyukan hukumomin na Larduna.Hakan ya sa, Kwalejin horarwa ya kasance abinda aka amince da shi wajen tsarin ilimi wanda ya fi muhimmanci.
Abin dogaron mu
Bayan da aka samu‘yar turjiya dangane da wurin da yafi dacewa a kafa kwalejin, sai aka zabi Katsina a matsayin wurin da yafi dacewa fiye da garuruwan da suke kan hanyar jirgin kasa kamar Kaduna, wadda ta kasance hedikwatar mulki ce ta Lardunan Arewa.Akwai abubuwan da suka sa aka zabi Katsina.Da farko dai, Katsina an dade ana yi mata kallo wani muhimmin wuri ne na koyon karatu abinda yasa, akwai nisa da yawa daga hanyoyin Jirgin kasa ga kuma“ga kuma wasu abubuwa na Allah ya yi mata wata mu’ujiza da Turawan mulkin mallakar Ingila suke tsoro”.Sauran abubuwan da suka sa aka zabi Katsina sun hada da akwai maganar abinda ya shafi kudi. Domin shi baya bukatar abinda zai, sa a kashe kudade masu yawa wajen gina ginin dindindin.Sarin Katsina na wancan lokacin Muhammadu Dikko (1906-1944),ya bada wani wuri da aka gina shi da kasa wato wurin da daliban za su zauna domin yin karatu. Sai Clifford ya amince da wurin da ba za a biya kudade masu yawa ba ya amince aka bar Kwalejin a Katsina.Bugu da kari kuma Sarkin Katsina,Muhammadu Dikko ya nuna jajaircewar shi da kuma hakurin bada taimako ga lamarin ilimin da gwamnati take son yi.
Duk da yake dai ofishin mulkin mallakar basu nuna amincewarsu ba kan lamarin da ake bukatar su zuba jari na Fam dubu ashirin 20,000, (£20,000) da ake bukata na gina dakunan karatu na dindindin,ba tare da wani bata lokaci ba sai aka fara bada fam dubu hudu 4,000 (£4,000) saboda gine ginen da za a fara da kuma fam dari 500 (£500 ) saboda sayen kaya. Zuwa karshen shekarar 1921, sai aka bude makarantar da dalibai wadanda matasa ne domin kuwa ta wani bangaren da iyalansu suna tafiya a kasa ko kuma suna zuwa kan Dawaki daga dukkan Lardunan Arewa.
A jawabin da ya gabatar Clifford lokacin da aka bude Kwalejin horarwa ta Katsina ranar 5 ga Maris 1922 inda ya ce:
Dole ne matasan da za su samu horo a wannan Kwaleji, wadanda daga baya kuma su ne za su koyar a Lardin Katsina da kuma sauran Masarautu, ya dace su maida hankalinsu lokacin da ake koya masu.Su maida hankalinsu wajen abinda ake koya masu saboda wani babban aiki ne wajen koyar da wasu.
Kada kuma su yi watsi da lura da lamurran addininsu, ko kuma su manta da al’adunsu, da na kasarsu, kada kuma su yi watsi da al’adar yi ma nag aba ladabi da biyayya musamman ma ga iyayensu, ga kuma dukkan masu mukamai na mulki ga kuma tsofaffi.
Hakanan ba kawai abubuwan darussan da aka koya maku daga littattafai, har ma da dabi’u nagari, halaye masu kyau, da kuma ganin girma, domin kuwa abubuwan da aka koya a littafi ‘yan kadan ne idan aka ce za a kwatanta su da sauran.
Kowane matashi wanda ya sami horo anan shi ma a gaba za a kira shidomin ya horar da mutane da yawa. Ya kamata kowa ya tuna da cewar “Babu wani mutumin da za a ga girman sa sosai sai wanda ya koya wato samu horo kwarai, shi ma za a yi ma shi ladabi”
Lokacin da aka fara yin karatun, makarantar ta maida hankalinta ne kawai kan ‘ya’yan masu hali, wato kamar Sarakuna da kuma wadanda suke kusa da su an fada masu su tura’ya’yansu makaranta. Wasu daga cikinsu sun yi yayin da wasu kuma suyka ki amincewa su tura ‘ya’yan nasu.
Fara zamanin ‘yan kasa
A wancan lokacin, dukkan malaman Turawan Ingila ne.Sai dai kuma duk da hakan, mutane biyu ‘yan Afirka suna da mukami a makarantar. Malam Nagwamatse yana koyar da Larabci shi ne kuma matsayin mai kula da wurin kwanan dalibai. Bugu da kari kuma yana kulawa da wuraren da dalibai suke kwana da kuma da’arsu. A lokacin ko tsakiyar shekarar ne, Malam Bello Kagara ya samu aiki a makarantar kamar yadda Nagwamatse yake yana koyar da Larabci da karatun Alkur’ani.
Tsakanin shekarar 1931-1937 babu wani daga cikin wadanda suka yi Shugabancin Kwalejin yake da farin jinni a Kwalejin kamar Mista. G.A. J.Bieneman yake da shi. Bieneman shi ne Shugaban Kwalejin na farko shi ne kuma ya dora ta kan tafarkin Eton a Kwalejin horon Malamai ta Katsin. Sauran wadanda suka yi Shugabancin Kwalejin sun hada da, Trebor S.Phillips (1931-1934), William E. Nicholson (1934-1935)da kuma Eric Mort (1935-1946) suna daga cikin manyan jami’ai wadanda suka fara aiki a sashen kafin yakin duniya na daya.
Kwaleji mai zurfi ta Katsina: A shekarar 1929, an kara martabar makarantar daga Kwalejin horar da Malaman makaranta zuwa Kwalejin ilimi mai zurfi ta Katsina.An fara amfani ne da Kwalejin ilimi mai zurfi ta Katsina ranar 1 ga Afrilu 1931 hakan ne ya nuna irin tunanin da Gwamnatin Birtaniyya take yi dangane da Kwalejin. Masu kishin kan irin yadda Arewa ta ke kokarin ci gaba kan tafarkin ilimi ya sa an fara tunanin a maida Kwalejin zuwa ko kamar irin yadda Kudancin Nijeriya suka ci gaba kan tafarkin na ilimin na su wato nagartar da yake da ita. Bayan da Urling Smith ya yi ritaya, Eric R.J. Hussey ya gaje shi a matsayin matsayin sabon Darektan ilimi.
Bayan da aka ba Hussey aiki hakan ya sa aka fara yin wata sabuwar shawara ko kuma sabon tunani akan Kwalejin da kuma matsayin ilimi a Arewacin Nijeriya. Hussey ya bada shawarar yin gyara kan tafarkin ilimi a Lardunan Arewacin Nijeriya, wanda an tsara abin ne domin a gyara shi tsarin ilimi na Lardunan Arewacin Nijeriya ya zama daidai da na Lardunan Kudancin Nijeriya. Ita babbar Kwaleji ko Kwalejin ilimi mai zurfi ita ce za ta maye gurbin Kwalejin horarwa ta Katsina.
Babbar Kwaleji ko Kwalejin ilimi mai zurfi za ta samar da ilimin shekara biyu na gaba daya, sai kuma horarwa ta musamman da za a bada fifiko ko maida hankali kan mukaman gwamnati. Babbar manufar ita ce a samu Malaman makaranta, mataimaka kan ayyukan da suka shafi Asibitoci,da kuma Akawu. “Makarantar Midil da ita ce ake yi kafin makarantun Firamare za ta samar da karatu na shekara shida na karatu kan bangarorin ilimi, domin hakan ne ya sa Kwalejin ilimi mai zurfi ta Arewa ta kara bunkasa yadda ta ke, da zummar lamarin ya kasance tamkar yadda shi tafarkin ilimi ya ke a ko tsara yadda zai kasance a Yaba kusa da Legas.















Discussion about this post