ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Rayuwar Hon. Aminu Suleiman A Takaice

by Bello Hamza
5 months ago
Tarihin

Masu iya magana sun ce, “In ka ji wane ba banza ba, in ba’a sha ruwa ba, an sha rana”

Hon. Aminu Suleiman shi ne Shugaban shahararriyar kungiyar magoya bayan Shugaba Tinubu mai suna “Tinubu Support Organisation (TSO)”. Shi ne ya kirkiro kungiyar kimanin shekaru Shida kafin Shugaba Tinubu ya furta maganar yin takarar Shugaban kasa domin nuna kauna ga shugaban da yada Manufofinsa na yin Takarar Shugabancin Nijeriya kasancewarsa mutumin da ya san halaye da dabi’un Shugaba Tinubu tun yana Gwamnan Jihar Legas.

  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Shi mutum ne zakakuri, jajirtacce, haziki mai kokari da himmar neman na kansa tun yana matashi. Yana da kokarin kamanta gaskiya da rikon amana. Yana da biyayya da da’a ga magabatansa da bin umarnin shugabanninsa a kodayaushe

ADVERTISEMENT

Tarihin rayuwar Hon. Aminu Suleiman ya nuna cewa mutum ne wanda ya shafe kusan shekaru Talatin yana fafatawa da gwagwarmaya a aiyukan kwangila, safara, harkar mai da cinikaiya a sana’oi daban-daban a manyan biranen kasar nan tun daga lokacin mulkin soja har aka koma mulkin Dimokaradiyya. Bugu da kari, sabanin abun da wasu ke tunani, zuri’ar gidansu Hon. Aminu Suleiman na da rufin asiri, wanda sun mallaki kamfanin da ke hada-hadar mai, mai suna Bulasawa Petroleum wanda ya dade yana ta’ammalin cinikaiyar mai da Majalissar dokokin Nijeriya . Wannan na nuna cewa ba yau ya saba ganin kudi ko juya kudi ba.

Haka zalika, ya fara harkokin aiki a kamfanin Nasco a Legas tun 1991, lokacin mulkin Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida. Sannan a lokacin mulkin Jenar Sani Abacha ma ya yi kwangiloli a kamfanin mai na NNPC, ya yi kwangilar gina Rijiyoyin birtsatse a rukunin gidajen NNPC da ke Abuja a lokacin da Marigayi Bar. Haruna Abubakar ke MD na PPMC

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

A lokacin da Hon. Aminu Suleiman ke zama a Legas, Wani mutumin Maiduguri mai suna Gwani Askira mazaunin Titin Abiola Crescent shi ne ya hada Hon. Aminu Suleiman da Marigayi Mashood Abiola ya gabatar da kansa gare cewa shi mutumin Kebbi ne kuma yana goyon bayan siyasarsa, daga nan suka saba, suka yi harkokin siyasa na wani lokaci har aka yi zabe ya fadi, sai ya dawo Abuja a shekara ta 1999 daga Abuja ya sake komawa Legas da Shugaba Tinubu ya zama Gwamnan Legas ya ci gaba da huddar arziki da shi ya zama dan cikin gida a gidan Shugaba Tinubu ya saba da iyalinsa da makarraban Gwamnatinsa, alaka tsakanin Shugaba Tinubu Gwamnan Legas a wancan lokacin da Hon. Aminu Suleiman ta zama tamkar ta Da da Uba,har daga bisani ya kirkiro kungiyar TSO ta girma, ta karbu a idon duniya, ta kuma ba da gudunmawa mai tasiri a zaben 2023 Shugaba Tinubu ya zama Shugaban kasa

Bayan kasancewar Tinubu zababbbe shugaban kasa, Hon. Aminu Suleiman bai sami kowanne irin mukami ba sai bayan shekara, Shugaba Tinubu ya bashi mukamin Shugaban Majalissar zartarwa na kwalejin fasahar kimiyya da ke jihar Nasarawa, sannan bayan watanni ya sake bashi mukamin Dan Majalissar zartarwa na sabuwar hukumar Raya shiyar Arewa maso yammacin Nijeriya. Idan aka duba za a ga cewa tagwayen mukaman da ya samu a sabbin ma’aikatu ne wanda ke bukatar lokaci da aiki kafin harkokinsu su daidata. Kwatsam sai ga wani abun mamaki mai kama da almara, wata kungiya da baaa san tushenta ba wai ” Concern TSO Pressure Proups” na kalubalantar Hon. Aminu Suleiman cewa ya yi watsi da Yayanta da samarwa kansa mukamai kuma kungiyar bata tabuka komai ga Yayanta ba.

Abun tambaya a nan shi ne suwa a ka yi watsi da su? Kuma ta yaya mutum zai bai wa kansa mukami kuma yaushe aka ba da mukamin kuma da aka ba da mukaman wanne aiki aka yi a ma’aikatun kuma me aka samu da har za a makance a yi suka ko korafi? Idan kuma akwai wanda yake da shedar cewa Honourable ya karbi wani kudi, to ya kawo sheda ko ya baiyana ta ga jama’a. Maganar gaskiya ita ce har yanzu a hukumar raya shiyar Arewa maso yammacin Nijeriya ba a saki kudi an yi wani takamaiman aikin da shugabanninta za su sami kudi ba. Kai ko harkokin daukar ma’aikata ba’a fara ba. Haka zalika a Kwalejin fasahar Keana nan ma ba magana, yanzu ake gina asalin filin makarantar na dindindin da maganar daukar daliban farko da fara sabon zangon karatu na farko a makarantar.

La’akari da haka,in dai ba hassada, kyashi da da bakinciki ake ba, za a gane cewa babu wani takamaiman aiki muhimmi da ma’aikatun ke yi wanda har wasu za su fara zargin ana samun wani abu ko an yi wani abu ba tare da su ba. Babu shakka, Duk wani yunkuri na suka ko korafi na nuna cewa lallai wannan mutane ba cikakkun ‘yan kungiyar TSO ba ne. Saboda tun daga zaben 2023 da Tinubu ya samu nasara kungiyar bata huta ba, tana ci gaba da ayyukanta yadda ta saba a cikin gida da wajen Nijeriya kuma tana samun nasarori.

A karshe akwai wasu zarge-zarge marasa tushe ballantana makama da bai kamata mu ce uffan akansu ba, saboda suna nuni da masu wadannan zarge-zarge ba asalin ‘yan kungiyar ba ne, in kuma har ‘yayanta ne, to sun yi nisa da ita kuma basa bibiyar harkokinta ka’in da na’in, sun koma gefe daya suna surutai marasa amfani da kokarin hana ruwa gudu da bata aikin da shugabanta da sauran Jajirtattun ‘yan kungiyar masu da’a da yi mata hidima ba dare ba rana ke yi.

Tarihin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Matar Da Ta Haifi ‘Ya’ya Hudu Lokaci Guda Na Tsaka Mai Wuya A Kano

Matar Da Ta Haifi ‘Ya’ya Hudu Lokaci Guda Na Tsaka Mai Wuya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.