Shugaban Amurka, Donald Trump, ya janye jakadan ƙasar a Nijeriya, Richard M. Mills Jr., tare da wasu manyan jami’an diflomasiyya 29 da ke riƙe da muƙaman jakadu da muhimman mukamai a ofisoshin jakadanci a sassa daban-daban na duniya.
Jakada Mills, wanda aka naɗa a ranar 25 ga Yulin 2024, na daga cikin jakadu 13 da ke aiki a ƙasashen Afirka, da wannan mataki ya shafa inda wasu majiyoyi a birnin Washington, suka bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin sauya fasalin manufofin harkokin wajen Amurka bisa tsarin “Amurka Farko” na Trump.
- Trump Ya Yi Alƙawarin Dakatar da Shigowar Masu Hijira Daga Matalautan Ƙasashe
- Trump Na Murna Sosai Da Samar Da Matatar Manmu – Dangote
Rahoton kamfanin dillancin labarai na Associated Press (AP), ya ce an sanar da jami’an da abin ya shafa cewa wa’adin aikinsu zai ƙare a watan Janairun 2026, wanda dama daga cikinsu an naɗa su ne tun a gwamnatin Biden, amma suka ci gaba da aiki har zuwa farkon wa’adin Trump.
Wasu Jami’ai da suka nemi a sakaya sunayensu, sun bayyana cewa ba a kore su daga aikin diflomasiyya ba, sai dai kawai za a sauya musu muƙamai idan sun zaɓi ci gaba da yi wa ƙasar aiki, duk da cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ƙi bayyana adadin jakadun da matakin ya shafa, amma ta kare matakin da cewa “tsari ne na al’ada a kowace gwamnati.”
Nahiyar Afirka ce wannan lamari ya fi shafa, inda aka janye jakadu daga ƙasashe 13 ciki har da Nijeriya, wanda hakan na daga cikin manyan sauye-sauyen diflomasiyya da gwamnatin Trump, ta aiwatar tun bayan fara wa’adinta na biyu.














