Hukumar Gudanarwa ta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kogi (Kogi State Polytechnic), Lokoja, ta amince da sallamar wasu ma’aikata biyu bisa laifuffuka daban-daban. A cikin wata sanarwa da Daraktan hulɗa da Jama’a da Ladabtarwa, Uredo Omale, ya fitar, an ce an sallami Mukhtar Muhammed, jami’in gudanarwa mataki na biyu, sakamakon samunsa da laifin cin zarafin jima’i, yayin da aka sallami Funmilayo Afolabi, Mataimakiyar Babban Jami’in Gudanarwa, saboda gudun aiki na tsawon watanni tara.
Sanarwar ta ce Majalisar ta kuma amince da rage muƙamin Audu Mathew, Mataimakin Rijista, zuwa Babban Mataimakin Rijista saboda sakaci wajen aiki. Haka kuma, Majalisar ta amince da ɗaga darajar Malamai manya 11 zuwa matsayin manyan Malamai (Chief Lecturers), tare da haɓaka darajar ma’aikata 572 na koyarwa da na gudanarwa a cibiyar.
- Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
- Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano
Waɗannan matakai sun fito ne daga taron Majalisar Gudanarwa karo na 72, wanda Shugabanta, Barista Sani Shaibu, ya jagoranta a ranar Juma’a, 19 ga Disamba. Daga cikin waɗanda aka ɗaga matsayi akwai malamai daga makarantu daban-daban na kimiyya, da injiniya, da kasuwanci, da sadarwa, tare da amincewa da ƙarin haɓaka darajar ma’aikata 49 na koyarwa da 71 na gudanarwa a shekarar 2024, da kuma 225 na koyarwa da 227 na gudanarwa a shekarar 2025.
A jawabinsa, shugaban na Kwalejin, Farfesa Salisu Ogbo Usman, ya ce matakan na nuna ƙudurin Majalisar wajen tabbatar da ladabi, da gaskiya da ingancin ilimi. Ya kuma bayyana gano wani gungun masu ƙirƙirar sakamakon jarrabawa, inda aka kama Henry Tope da takardun sakamako 30 da shaidar kammala karatu guda ɗaya na bogi. Shugaban Majalisar, Barista Sani Shaibu, ya jaddada cewa Kwalejin ba za ta lamunci duk wani abu da zai ɓata mutuncinta ba, tare da kira ga ma’aikata su bi ƙa’idoji da ɗabi’un sana’a.














