ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Yadda Gwamnoni Ke Kafa Rundunonin Tsaro A Jihohinsu

by Sulaiman
6 months ago

Kalubalen tsaro a duk fadin Nijeriya, ba wani abu ba ne sabo, sai dai addu’ar Allah ya kawo sauki. 

 

Masu sharhi kan harkokin tsaro, na fashin baki da cewa, gwamnatin tarayya na yin iya kokarinta amma akwai bukatar ta sauya dabarun yaki da masu aikata muggan laifuka da suka hada da fashi da makami, garkuwa da mutane, ra’ayin riƙau, safarar miyagun kwayoyi da dai sauransu.

ADVERTISEMENT
  • Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Kammala Zaman Zaunannen Kwamitinta
  • An Samu Manyan Nasarori A Kannywood A ‘Yan Shekarun Nan –Maryan CTB

A yunƙurin da ake yi na ganin an shawo kan ƙalubalen tsaro, wasu gwamnoni a Kudanci da Arewacin Nijeriya, sun fara kaddamar da rundunar tsaro karkashin ikonsu don karfafa jami’an tsaro da ke ƙarƙashin ikon gwamnatin tarayya wajen shawo kan ƙalubalen tsaro da ya dabaibaye sassan ƙasar.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

A makon da ya gabata, gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da rundunar tsaro wacce za ta sanya ido kan al’ummomin jihar a ranar Talata, 23 ga watan Disamba, 2025 a filin wasa na Sani Abacha, Kano.

 

Sabbin rundunar da aka kafa sun kunshi jami’ai 2,000 da aka zaƙulo a kananan hukumomi 44 na jihar, ciki har da mata 130 da maza 1,870, domin karfafa tsaro da tattara bayanan sirri a jihar.

 

Gwamna Yusuf ya sanar da cewa, za a samar wa rundunar kayan aiki isassu yadda za ta kasance cikin shiri don tunkarar masu aikata manyan laifuka, ciki har da fashi da makami, ta’ammuli da miyagun kwayoyi, ‘yan daba, da sauran laifukan da ke barazana ga tsaron jama’a a birane da karkara.

 

A wannan rana, takwaran Gwamna Yusuf na jihar Filato, a wani sabon yunkuri na ƙarfafa yanayin tsaro domin samar da ingantacciyar zaman lafiya a faɗin Jihar, Gwamnan Caleb Manasseh Mutfwang, ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na tabbatar da zaman lafiya da tsaro, yana mai bayyana tsaro a matsayin “tushen da ake gina ci gaba mai ɗorewa a kai.”

 

Gwamna Mutfwang ya yi wannan sanarwar ne a ranar Talata, 23 ga Disamba, 2025, a filin wasa na Zaria Road, Jos, yayin bikin yaye jami’an rundunar tsaro mai suna ‘Rainbow’ su 1,450, da ke da alhakin taimakawa harkokin tsaron jihar domin fatattakar masu aikata muggan laifuka da ‘yan ta’adda dake addabar al’ummar jihar.

 

In ba a manta ba, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya kaddamar da rundunar kare al’umma (CPG), wadda aka fi sani da Askarawan Zamfara. Wannan wani gagarumin ci gaba ne wajen magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta

 

Askarawan su 2,645 an ya ye kashin farko ne a 1 ga Fabrairun, 2024.

 

Har ila yau, Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, a ranar Talata, 10/10/2023 ya kaddamar da rundunar kula da al’umma don karawa kokarin manyan hukumomin tsaro karfi a yaki da ‘yan fashi da makami a jihar.

 

Yayin da yake kaddamar da rukunin farko na rundunar, Radda ya ce hakan wani ɓangare ne na kokarin gwamnatinsa na daukar hanyar haɗa hannu da al’umma don magance rashin tsaro a jihar.

 

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Ibrahim Kaula, ya fitar, rukunin farko na rundunar ya kunshi matasa 2,400 da aka zaba daga kananan hukumomi 34 na jihar.

 

Bugu da kari, akwai wata rundunar tsaro ta hadin gwiwa mai suna Amotekun – wata runduna ce ta tsaro ta yankin Kudu maso Yammacin Nijeriya, wadda jihohin Yarbawa shida (Lagos, Ogun, Oyo, Ondo, Ekiti, Osun) suka kafa don magance matsalar rashin tsaro kamar garkuwa da mutane, da fashi da makami, da kuma kare manyan hanyoyi/dazuzzuka.

 

An ƙaddamar da ita a watan Janairun 2020, kuma ita ce runduna ta farko ta tsaro a yankin Nijeriya, wacce aka kafa a Ibadan, Jihar Oyo.

 

Wannan yunkurin da gwamnonin jihohi ke yi wurin ganin an kawo karshen taɓarɓarewar tsaro da ya baibaye kasar, na nuna cewa, lallai Akwai buƙatar sojoji da ‘yansanda su sauya dabarun yaki da masu aikata manyan laifuka, musamman ‘yan bindiga dake kashe al’umma ba tare da wani dalili ba.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Next Post
Kasashen Afirka 10 Da Suka Fi Fuskantar Juyin Mulki

Kasashen Afirka 10 Da Suka Fi Fuskantar Juyin Mulki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.