ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsayuwa Da Ƙafa Biyu Ya Fi Tsayuwa Da Kafa Ɗaya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
Tsayuwa

Lokacin da na karbi ragamar aiki a matsayin Ministan Tsaro, na yi alkawarin karfafa tsarin tsaron kasar. Na jaddada cewa, da farko, a matsayinmu na ‘yan Nijeriya dole ne mu dauki alhakin daukar nauyin da kalubalen da kasarmu ke fuskanta.

 

Wannan ba kawai magana ba ce, illa kira ne zuwa aiki. Ina kuma tsaye daram wajen tabbatar da cewa mun fuskanci kalubalen tsaronmu kai tsaye ta hanyar amfani da falsafar “hadin kai da manufa daya”, wadda ke nufin mu yi aiki tare a matsayin kungiya guda, maimakon kowanne bangare ya yi aiki shi kadai kamar rundunar da ke zaman kanta. ”

ADVERTISEMENT

 

“Wannan ita ce falsafar da na bi a duk tsawon aikina na hidimta wa kasa a mukaman jagoranci da na ma’aikata a cikin aikin sojin Nijeriya. Wannan tunani ya ci gaba da kasancewa tare da ni har zuwa yau.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

 

Na kuma saba da bai wa jami’ai kwarin gwiwa da ke karkashina su fahimci muhimmancin wannan tunanin na dabarun tsaro, tare da aiwatar da shi a duk inda suka tsinci kansu a cikin aikinsu.

 

Matsayin da nake rike da shi a yau yana da nufin karfafa tsarin tsaron kasar, bisa ga umarnin da Bola Ahmed Tinubu, Babban Kwamandan Askarawan Nijeriya, ya ba ni.

 

Ina da cikakken kuduri da himma wajen mayar da fata da burin ‘yan Nijeriya su zama gaskiya ta hanyar kawo karshen ta’addanci a kasar.”

 

Daidaitawar Soji Da Farar Hula

“A lokacin da nake hidima a matsayin jami’in soja, daya daga cikin kalubalen da na fuskanta shi ne daidaita tunanin soja da al’adun farar hula. Akwai lokuta da dama da dole ne mutum ya saurari ra’ayin farar hula wajen magance matsalolin tsaro yayin da suke faruwa.

 

A lokutan da na bi ra’ayin farar hula, na ga sakamakon da na samu a matsayin kwamanda ya burge ni matuka. Duk da na san cewa wasu daga cikin shawarar da na yanke ba su yi wa wasu daga cikin sojojina dadi ba, amma a matsayina na kwamanda, dole ne su amince da hukuncin da na yanke.

 

A koyaushe ni nake daukar alhakin wadannan shawarwari. Idan na waiwaya baya yanzu, ina farin ciki da na yanke wadannan matakai domin sun tabbatar da cewa suna da amfani sosai.”

 

Haramtaccen Yaki Da Ingantacce

Yakin da bai da daidaito ba za’a auna shi da yawan ‘yan ta’adda da aka kashe a daji kawai ba, amma da yawa akwai mutanen da aka ‘yanto daga shiga ta’addanci ko aka fito da su daga daji. Wannan yana nuna juriya a yaki, wato daga kirga gawarwaki zuwa halastaccen mulki.

 

Yakin da ‘yan ta’adda ke yi yana da wahala kuma sau da yawa yana taba yunkurin dakaru ne kawai, wanda hakan zai kai ga jama’a su gaji da jinkirin samun sakamako. Amma halattaccen yaki yana mai da hankali kan gano tushen matsalolin da ke haddasa rikicin. Saboda haka, dabarun aikina sun ginu ne a kan hada wadannan hanyoyi biyu domin samun sakamako mai dorewa.

 

Nadin da aka yi min daga baya a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS) ya ba ni damar fadada gano abin da ake kira “tsarin Borno” a cikin ayyukan soji..

 

Ina tuna cewa a lokacin da nake CDS, a taron Kwamandojin Rundunar Hadin Gwiwa na CDS mai taken Inganta hadin Kai A Sansanin Soji”, na jaddada muhimmancin hadin kai wajen aiki, amfani da dabaru, da kuma hada al’umma baki daya wajen magance matsalolin tsaro.

 

Misali, canza sunan aikin hadin gwiwar soja a Jihar Filato daga ‘Operation Safe Haben’ zuwa ‘Operation Enduring Peace’ wanda an yi shi ne domin samar da sabon hangen nesa ga sojoji da al’ummomin yankin kan muhimmancin yin aiki tare domin samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar Filato.

 

Ina alfahari da cewa wannan dabarar tana aiki a jihar da kuma a sauran wuraren da sojojin Nijeriya ke gudanar da ayyukansu a fadin kasar.

 

Dabarun Hada Kan Al’umma

Akwai wani abu da na fahimta wanda nake son jaddadawa. Ba kasafai ake ganin sa a fili a cikin al’umma. A halin yanzu muna yaki ne da rikici mai sassa da dama. Kungiyoyin ta’addanci kamar Boko Haram, ISWAP, da Lakurawa da wasu kungiyoyin masu tashin hankali sun hada kai, sun ajiye sabanin da ke tsakaninsu domin su yi aiki tare su kai hare-hare. A wasu lokuta ma suna musayar bayanan sirri a tsakaninsu.

 

Wannan gaskiya ce, kuma shi ya sa ake bukatar abin da ake kira “tsayuwa da kafafu biyu”, wato hada dabarun karfi na soja da kuma dabarun da ba na soja ba a cikin ayyukan tsaronmu, domin samar da daidaito da ake bukata wajen kayar da ta’addanci.

 

Idan kungiyoyin ta’addanci na iya hada kai, me zai hana jama’ar kasa su hada kai da sojoji? Ba za mu iya kayar da ta’addanci da bindigogi da harsasai kawai ba. Wannan shi ne ainihin sakon da nake son isarwa a wannan rubutu.

 

Kwarewata a matsayin Kwamandan Yanki da Babban Hafsan Tsaro har yanzu tana da tasiri sosai a tunanina. Na kalli matsalolin daga matsayi na jagoranci da na ma’aikata. Misali, yanke shawarar bin ra’ayin farar hula ta hanyar yin hadin kai ba tare da tangarda ba da gwamnatin Jihar Borno ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addancin Boko Haram.

 

Wannan kuma yana karfafa hujjata ta cewa tsaro nauyi ne da kowa ke dauka. Wannan shi ne tsarin aiki a kasashen da suka ci gaba. Ban yarda cewa tsarinmu ya kamata ya bambanta ba.

 

Wannan shi ne tsarin da Ma’aikatar Tsaro ke aiwatarwa. Ina farin cikin ganin cewa dukkan sassan sojojin Nijeriya sun daidaita da wannan dabarar. Haka kuma ma’aikatar tana yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma, cibiyoyin addini da na gargajiya, kafofin yada labarai, kungiyoyin farar hula, da sassan kasuwanci na musamman domin shiga cikin dabarar “Hadin Kan Al’umma Gaba daya” wajen magance kalubalen tsaro na kasa.

 

Mun tsara wani samfurin aika sako wanda ya dace da kowane matsayi na al’umma, har ma da mazauna karkara. Manufar ita ce samar da wayar da kai cewa idan muka hada kai, za mu iya kai da ta’addanci kasa idan muka dage a kan hakan.

 

Akwai abubuwa da dama da ke haifar da rashin tsaro, amma akwai hanya daya da za ta iya dakatar da shi. Kuma wannan hanya ita ce lokacin da ’yan Nijeriya suka dauki nauyin hakan, ba tare da la’akari da al’adu ko qabila ba. Wannan nauyi ne na tilas domin juya yanayi a kan wadanda ba sa fatan alheri ga kasarmu.

 

‘Yan Kallo Da Ba Sa Kawo Dauki

Kwanan nan na gabatar da jawabi na musamman a taron shekara-shekara na Kungiyar Tsoffin Daliban Kwalejin Tarayya ta Kaduna a matakin duniya. Na jaddada cewa:

 

“Tarihi yana koya mana cewa babu wata kasa da za ta kasance mai tsaro idan ’yan kasarta suna zama masu kallo da ba sa shiga tsakani.”

 

Na ba da misali cewa manomi a Sakkwato, mai kasuwanci a Legas, da malami a Enugu suna zama layin farko na tsaro a kasa. Wannan yana kama da motsa muhawara kan tsaro daga sansanonin soja zuwa tituna, yana nuna cewa tsaro nauyi ne da ke wuyan kowa. Sojoji ba za su iya kasancewa a ko’ina ba. Saboda haka, ya zama dole ’yan Nijeriya su kasance masu shiga tsakani cikin tsarin tsaro, ba masu kallo marasa shiga tsakani ba.

 

Wannan rubutu na zaba masa take mai sauki wato “Tsayuwa da kafafu biyu ya fi tsayuwa da kafa daya”. Wannan dabara ce da ta dace da sabon tunani da muke kokarin gabatarwa.

 

Ina son sakon ya kai ga kowa, daga mai POS a Ibadan, mai dinki a Kaduna, har zuwa ma’aikacin gwamnati a Port Harcourt. Wannan wajibi ne, kuma yana dauke da alkawari zuwa ga ’yan Nijeriya na “tsayuwa da kafafu biyu” a yaki da ta’addanci.

 

Na dauki wannan alkawari ne a ranar 21 ga Satumba, 1991, lokacin da aka ba ni Kwamishinan Shugaban Kasa don aiki a Rundunar Sojan Nijeriya a matsayin jami’in soja na kasa. Dole ne mu hada kai don canza al’adar tsaro ta kasa.

Tsayuwa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Tsayuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Tsayuwa
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Tsayuwa
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
gombe

Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.