ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya

by Sani Anwar
3 weeks ago

Gwamna Hope Uzodinma, ya yi gargaɗin cewa; dimokuraɗiyyar Nijeriya, na iya fuskantar babbar barazana da haɗari, idan jam’iyyun adawa suka kasa gina manyan tsare-tsaren da za su ƙalubalanci jam’iyyar APC mai mulki, gabanin babban zaɓen 2027.

Uzodinma, ya yi magana ne a ranar Asabar a yayin zaɓen fid da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, inda shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya samu tikitin takara a jam’iyyar, don sake tsayawa a karo na biyu, ba tare da ƴan adawa ba.

Gwamnan na Imo ya ce, dimokuraɗiyya na samun bunƙasa ne ta hanyar hamayya, yana mai jaddada cewa; rashin samun sahihin ɗan adawa na iya raunana  dimokuraɗiyyar ƙasar.

ADVERTISEMENT

“Babu dimokuraɗiyya, idan babu ƴan adawa, ina ƙarfafa gwiwar jam’iyyun adawa da su yi aiki tuƙuru kamar yadda jam’iyya mai mulki ta yi, wanda hakan wataƙila zai iya bas u dama a nan gaba,” in ji Uzodimma.

Gwamnan ya kuma yi alfahari da cewa, nuna ƙarfi da yin abin da ya kamata na jam’iyyar APC, ya sanya jam’iyyar samun ƙarfi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Idan ka lura da abin da ke faruwa a matakin ƙasa, yadda aka zaburar da jama’a, tun daga batun yin rajistar shiga jam’iyya, wanda aka yi ta hanyar na’urar intanet, har zuwa tabbatar da mambobin ƙungiyar, za ka ga yadda kimanin mutum 35,000 a kowace mazaɓa guda a dukkanin ƙananan hukumomi suka yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Hakan na nufin, idan dukkan ƴan jam’iyyarmu suka zaɓi shugaba Bola Tinubu, ya riga ya lashe zaɓen”.

Uzodimma ya danganta yawan fitowar jama’a da aka samu a lokacin zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar APC da abin da ya bayyana a matsayin hada-hadar jama’a da gangan da aka ɓullo da ita ta hanyar yin rajistar shiga jam’iyyar ta dijital.

Gwamnan ya ƙara yaba wa salon jagorancin Tinubu, inda ya jaddada cewa; shugaban ƙasa ya yi abin da ya dace da ya cancanci a sake zaɓarsa a karagar mulki.

“Shugaba Bola Tinubu, ya yi abin da ya dace ya sake komawa a karo na biyu, ina so in taya shi murna da ya ɗauki lokaci ya yi siyasa yadda ya kamata,” in ji Uzodimma.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.