ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya

by Sani Anwar
4 days ago

Gwamna Hope Uzodinma, ya yi gargaɗin cewa; dimokuraɗiyyar Nijeriya, na iya fuskantar babbar barazana da haɗari, idan jam’iyyun adawa suka kasa gina manyan tsare-tsaren da za su ƙalubalanci jam’iyyar APC mai mulki, gabanin babban zaɓen 2027.

Uzodinma, ya yi magana ne a ranar Asabar a yayin zaɓen fid da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, inda shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya samu tikitin takara a jam’iyyar, don sake tsayawa a karo na biyu, ba tare da ƴan adawa ba.

Gwamnan na Imo ya ce, dimokuraɗiyya na samun bunƙasa ne ta hanyar hamayya, yana mai jaddada cewa; rashin samun sahihin ɗan adawa na iya raunana  dimokuraɗiyyar ƙasar.

ADVERTISEMENT

“Babu dimokuraɗiyya, idan babu ƴan adawa, ina ƙarfafa gwiwar jam’iyyun adawa da su yi aiki tuƙuru kamar yadda jam’iyya mai mulki ta yi, wanda hakan wataƙila zai iya bas u dama a nan gaba,” in ji Uzodimma.

Gwamnan ya kuma yi alfahari da cewa, nuna ƙarfi da yin abin da ya kamata na jam’iyyar APC, ya sanya jam’iyyar samun ƙarfi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Idan ka lura da abin da ke faruwa a matakin ƙasa, yadda aka zaburar da jama’a, tun daga batun yin rajistar shiga jam’iyya, wanda aka yi ta hanyar na’urar intanet, har zuwa tabbatar da mambobin ƙungiyar, za ka ga yadda kimanin mutum 35,000 a kowace mazaɓa guda a dukkanin ƙananan hukumomi suka yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Hakan na nufin, idan dukkan ƴan jam’iyyarmu suka zaɓi shugaba Bola Tinubu, ya riga ya lashe zaɓen”.

Uzodimma ya danganta yawan fitowar jama’a da aka samu a lokacin zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar APC da abin da ya bayyana a matsayin hada-hadar jama’a da gangan da aka ɓullo da ita ta hanyar yin rajistar shiga jam’iyyar ta dijital.

Gwamnan ya ƙara yaba wa salon jagorancin Tinubu, inda ya jaddada cewa; shugaban ƙasa ya yi abin da ya dace da ya cancanci a sake zaɓarsa a karagar mulki.

“Shugaba Bola Tinubu, ya yi abin da ya dace ya sake komawa a karo na biyu, ina so in taya shi murna da ya ɗauki lokaci ya yi siyasa yadda ya kamata,” in ji Uzodimma.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tsadar Kuɗin Ganin Likita Da Gwaje-gwaje Sun Sa Mutane Ƙaurace Wa Asibitocin Gwamnati

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.