ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya

by Sani Anwar
2 months ago

Gwamna Hope Uzodinma, ya yi gargaɗin cewa; dimokuraɗiyyar Nijeriya, na iya fuskantar babbar barazana da haɗari, idan jam’iyyun adawa suka kasa gina manyan tsare-tsaren da za su ƙalubalanci jam’iyyar APC mai mulki, gabanin babban zaɓen 2027.

Uzodinma, ya yi magana ne a ranar Asabar a yayin zaɓen fid da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, inda shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya samu tikitin takara a jam’iyyar, don sake tsayawa a karo na biyu, ba tare da ƴan adawa ba.

Gwamnan na Imo ya ce, dimokuraɗiyya na samun bunƙasa ne ta hanyar hamayya, yana mai jaddada cewa; rashin samun sahihin ɗan adawa na iya raunana  dimokuraɗiyyar ƙasar.

ADVERTISEMENT

“Babu dimokuraɗiyya, idan babu ƴan adawa, ina ƙarfafa gwiwar jam’iyyun adawa da su yi aiki tuƙuru kamar yadda jam’iyya mai mulki ta yi, wanda hakan wataƙila zai iya bas u dama a nan gaba,” in ji Uzodimma.

Gwamnan ya kuma yi alfahari da cewa, nuna ƙarfi da yin abin da ya kamata na jam’iyyar APC, ya sanya jam’iyyar samun ƙarfi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Dora Takardun Pantami A Shafin Hukumar INEC

Rikicin Tikitin Takarar Gwamnan ADC A Kaduna: An Buƙaci Ashiru Kudan Ya Dakatar da Naɗin Mataimaki

Idan ka lura da abin da ke faruwa a matakin ƙasa, yadda aka zaburar da jama’a, tun daga batun yin rajistar shiga jam’iyya, wanda aka yi ta hanyar na’urar intanet, har zuwa tabbatar da mambobin ƙungiyar, za ka ga yadda kimanin mutum 35,000 a kowace mazaɓa guda a dukkanin ƙananan hukumomi suka yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Hakan na nufin, idan dukkan ƴan jam’iyyarmu suka zaɓi shugaba Bola Tinubu, ya riga ya lashe zaɓen”.

Uzodimma ya danganta yawan fitowar jama’a da aka samu a lokacin zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar APC da abin da ya bayyana a matsayin hada-hadar jama’a da gangan da aka ɓullo da ita ta hanyar yin rajistar shiga jam’iyyar ta dijital.

Gwamnan ya ƙara yaba wa salon jagorancin Tinubu, inda ya jaddada cewa; shugaban ƙasa ya yi abin da ya dace da ya cancanci a sake zaɓarsa a karagar mulki.

“Shugaba Bola Tinubu, ya yi abin da ya dace ya sake komawa a karo na biyu, ina so in taya shi murna da ya ɗauki lokaci ya yi siyasa yadda ya kamata,” in ji Uzodimma.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

MASU ALAKA

Siyasa

PDP Ta Dora Takardun Pantami A Shafin Hukumar INEC

July 30, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

Rikicin Tikitin Takarar Gwamnan ADC A Kaduna: An Buƙaci Ashiru Kudan Ya Dakatar da Naɗin Mataimaki

July 30, 2026
Zaben Neja: APC Ta Yi Nasara A Kananan Hukumomi 22 Daga Cikin 25 
Siyasa

APC Ta Musanta Rahotannin Tashin Hankali A Taron Masu Ruwa da Tsaki A Delta

July 29, 2026
Next Post
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.