ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya

by Sani Anwar
1 month ago

Gwamna Hope Uzodinma, ya yi gargaɗin cewa; dimokuraɗiyyar Nijeriya, na iya fuskantar babbar barazana da haɗari, idan jam’iyyun adawa suka kasa gina manyan tsare-tsaren da za su ƙalubalanci jam’iyyar APC mai mulki, gabanin babban zaɓen 2027.

Uzodinma, ya yi magana ne a ranar Asabar a yayin zaɓen fid da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, inda shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya samu tikitin takara a jam’iyyar, don sake tsayawa a karo na biyu, ba tare da ƴan adawa ba.

Gwamnan na Imo ya ce, dimokuraɗiyya na samun bunƙasa ne ta hanyar hamayya, yana mai jaddada cewa; rashin samun sahihin ɗan adawa na iya raunana  dimokuraɗiyyar ƙasar.

ADVERTISEMENT

“Babu dimokuraɗiyya, idan babu ƴan adawa, ina ƙarfafa gwiwar jam’iyyun adawa da su yi aiki tuƙuru kamar yadda jam’iyya mai mulki ta yi, wanda hakan wataƙila zai iya bas u dama a nan gaba,” in ji Uzodimma.

Gwamnan ya kuma yi alfahari da cewa, nuna ƙarfi da yin abin da ya kamata na jam’iyyar APC, ya sanya jam’iyyar samun ƙarfi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Idan ka lura da abin da ke faruwa a matakin ƙasa, yadda aka zaburar da jama’a, tun daga batun yin rajistar shiga jam’iyya, wanda aka yi ta hanyar na’urar intanet, har zuwa tabbatar da mambobin ƙungiyar, za ka ga yadda kimanin mutum 35,000 a kowace mazaɓa guda a dukkanin ƙananan hukumomi suka yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Hakan na nufin, idan dukkan ƴan jam’iyyarmu suka zaɓi shugaba Bola Tinubu, ya riga ya lashe zaɓen”.

Uzodimma ya danganta yawan fitowar jama’a da aka samu a lokacin zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar APC da abin da ya bayyana a matsayin hada-hadar jama’a da gangan da aka ɓullo da ita ta hanyar yin rajistar shiga jam’iyyar ta dijital.

Gwamnan ya ƙara yaba wa salon jagorancin Tinubu, inda ya jaddada cewa; shugaban ƙasa ya yi abin da ya dace da ya cancanci a sake zaɓarsa a karagar mulki.

“Shugaba Bola Tinubu, ya yi abin da ya dace ya sake komawa a karo na biyu, ina so in taya shi murna da ya ɗauki lokaci ya yi siyasa yadda ya kamata,” in ji Uzodimma.

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.