ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Dama Ce Ta Ragewa Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
1 month ago
Arsenal

Masu sharhi a kwallon kafa suna ci gaba da bayyana ra’ayinsu a kan halin da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal take ciki na yiwuwar rasa gasar firimiya ta Ingila bayan da Arsenal din ta sake tsintar kanta a wani yanayi na rashin tabbas a karshen kakar wasa duk da cewa ana ganin har yanzu Arsenal din tana da damar lashe gasar.

Duk da cewa ana ganin Arsenal din ba za ta iya ba, amma har yanzu magoya bayan Arsenal na ci gaba da alhinin rashin nasarar da kungiyar ta yi a wasanta da Manchester City na ranar Lahadi. Rashin nasarar da kungiyar ta yi da ci 2-1 ya sake jefa ta cikin babbar barazanar gaza lashe Kofin Premier da ta shafe fiye da shekara 20 tana kishirwarsa.

A shekarun baya-bayan nan kungiyar kan nuna alamun lashe kofin ta hanyar hawa teburin gasar tare da bayar da tazara mai yawa, amma ana zuwa karshen kakar sai komai ya sukurkuce mata. Hakan ce ma ta sa masu bibiyar kwallon kafa, musamman masu hammaya da ita ke yi mata kirari da ”Kofi Haram”.

ADVERTISEMENT

A wannan kaka kungiyar ta yi yunkurin goge wannan kirari, musamman ganin yadda ta jima a kan teburin gasar ta tazara mai yawa da ta bai wa City ta biyu. To sai dai da alama da wuya hakar kungiyar ta cimma ruwa, bayan shan kaye da 2-1 a hannun AFC Bournemouth da kuma 2-1 a hannun City, lamarin da ya rage tazarar makin da ke tsakaninsu zuwa uku, yayin da Manchester City ta je ta doke kungiyar kwallon kafa ta Burnley a kwantan wasan da take da shi kuma ya ba ta damar komawa mataki na daya.

A yanzu da ya rage wasa biyar a karkare gasar tambayar da mafi yawan masu bibiyar kwallon kafa ke yi ita ce ko Arsenal za ta iya karya bakin kirarin da ake yi mata na Kofi Haram? ko kuwa dai tarihi zai ci gaba da maimaita kansa?

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

A wajen magoya bayan Arsenal, watan Afrilu ya ci gaba da kasancewa wata mafi tsanani a wajensu. Alkaluma sun nuna cewa a wannan watan ne Arteta ke yawan rashin nasara a wasannin Premier, wani abu da alamu ke nuna cewa zai maimaita kansa a wannan shekarar ma, kasancewar ta yi rashin nasara biyu zuwa yanzu a cikin watan.

Wasu suna ganin akwai rashin kwarewa a wajen mai horarwa Mikel Arteta musamman ta juriya da mayar da hankali saboda ana ganin ba za a hada shi da Pep Guardiola ba wanda shi ne ya koya wa Arteta aiki kuma ya zama mataimakinsa a Manchester City kafin daga baya Arsenal din ta dauki Arteta ya koma mai horar da ‘yanwasanta.

A watan Afrilun shekarar 2021, Arsenal karkashin Arteta ta yi wasa hudu, inda ta ci daya kawai, ta yi rashin nasara biyu tare da kunnen doki daya.

Haka ma a Afrilun shekara ta 2022, kungiyar ta buga wasa 5, ta ci biyu daga ciki ta kuma yi rashin nasara uku. A Afrilun shekara ta 2023 ma, Arsnela ta buga wasa 5, inda ta ci guda daya tare da yin kunnen doki a uku da kuma rashin nasara daya.

To amma a shekara ta 2024, abubuwa sun sauya, inda ta buga wasanni 6, ta ci 5 daga ciki da rashin nasara daya. Amma a Afrilun 2025 da ya gabata sai aka sake komawa gidan jiya, inda ta buga wasa 5, ta ci 2 da kunnen doki 3.Sai dai duk da haka Arteta na da kwarin gwiwa, kamar yadda ya bayyana a taron manema labarai da ya gabatar bayan wasan da suka yi rashin nasara a filin wasa na Ettihad.

Arteta ya ce sun yi rashin nasara a wasa mai muhimmanci, amma har yanzu suna da kwarin gwiwa kuma suna da yakinin cewa za su lashe gasar ta bana.

Wasanni 5 da suka rage wa Arsenal

Newcastle United (Gida). Fulham (Gida). West Ham United (Waje). Burnley (Gida). Crystal Palace (Waje).

Wasanni 6 da suka rage wa City

Burnley (Waje). Eberton (Waje). Brentford (Gida). AFC Bournemouth (Waje). Crystal Palace (Gida). Aston Billa (Gida)

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.