ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Dama Ce Ta Ragewa Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
2 months ago
Arsenal

Masu sharhi a kwallon kafa suna ci gaba da bayyana ra’ayinsu a kan halin da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal take ciki na yiwuwar rasa gasar firimiya ta Ingila bayan da Arsenal din ta sake tsintar kanta a wani yanayi na rashin tabbas a karshen kakar wasa duk da cewa ana ganin har yanzu Arsenal din tana da damar lashe gasar.

Duk da cewa ana ganin Arsenal din ba za ta iya ba, amma har yanzu magoya bayan Arsenal na ci gaba da alhinin rashin nasarar da kungiyar ta yi a wasanta da Manchester City na ranar Lahadi. Rashin nasarar da kungiyar ta yi da ci 2-1 ya sake jefa ta cikin babbar barazanar gaza lashe Kofin Premier da ta shafe fiye da shekara 20 tana kishirwarsa.

A shekarun baya-bayan nan kungiyar kan nuna alamun lashe kofin ta hanyar hawa teburin gasar tare da bayar da tazara mai yawa, amma ana zuwa karshen kakar sai komai ya sukurkuce mata. Hakan ce ma ta sa masu bibiyar kwallon kafa, musamman masu hammaya da ita ke yi mata kirari da ”Kofi Haram”.

ADVERTISEMENT

A wannan kaka kungiyar ta yi yunkurin goge wannan kirari, musamman ganin yadda ta jima a kan teburin gasar ta tazara mai yawa da ta bai wa City ta biyu. To sai dai da alama da wuya hakar kungiyar ta cimma ruwa, bayan shan kaye da 2-1 a hannun AFC Bournemouth da kuma 2-1 a hannun City, lamarin da ya rage tazarar makin da ke tsakaninsu zuwa uku, yayin da Manchester City ta je ta doke kungiyar kwallon kafa ta Burnley a kwantan wasan da take da shi kuma ya ba ta damar komawa mataki na daya.

A yanzu da ya rage wasa biyar a karkare gasar tambayar da mafi yawan masu bibiyar kwallon kafa ke yi ita ce ko Arsenal za ta iya karya bakin kirarin da ake yi mata na Kofi Haram? ko kuwa dai tarihi zai ci gaba da maimaita kansa?

LABARAI MASU NASABA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

A wajen magoya bayan Arsenal, watan Afrilu ya ci gaba da kasancewa wata mafi tsanani a wajensu. Alkaluma sun nuna cewa a wannan watan ne Arteta ke yawan rashin nasara a wasannin Premier, wani abu da alamu ke nuna cewa zai maimaita kansa a wannan shekarar ma, kasancewar ta yi rashin nasara biyu zuwa yanzu a cikin watan.

Wasu suna ganin akwai rashin kwarewa a wajen mai horarwa Mikel Arteta musamman ta juriya da mayar da hankali saboda ana ganin ba za a hada shi da Pep Guardiola ba wanda shi ne ya koya wa Arteta aiki kuma ya zama mataimakinsa a Manchester City kafin daga baya Arsenal din ta dauki Arteta ya koma mai horar da ‘yanwasanta.

A watan Afrilun shekarar 2021, Arsenal karkashin Arteta ta yi wasa hudu, inda ta ci daya kawai, ta yi rashin nasara biyu tare da kunnen doki daya.

Haka ma a Afrilun shekara ta 2022, kungiyar ta buga wasa 5, ta ci biyu daga ciki ta kuma yi rashin nasara uku. A Afrilun shekara ta 2023 ma, Arsnela ta buga wasa 5, inda ta ci guda daya tare da yin kunnen doki a uku da kuma rashin nasara daya.

To amma a shekara ta 2024, abubuwa sun sauya, inda ta buga wasanni 6, ta ci 5 daga ciki da rashin nasara daya. Amma a Afrilun 2025 da ya gabata sai aka sake komawa gidan jiya, inda ta buga wasa 5, ta ci 2 da kunnen doki 3.Sai dai duk da haka Arteta na da kwarin gwiwa, kamar yadda ya bayyana a taron manema labarai da ya gabatar bayan wasan da suka yi rashin nasara a filin wasa na Ettihad.

Arteta ya ce sun yi rashin nasara a wasa mai muhimmanci, amma har yanzu suna da kwarin gwiwa kuma suna da yakinin cewa za su lashe gasar ta bana.

Wasanni 5 da suka rage wa Arsenal

Newcastle United (Gida). Fulham (Gida). West Ham United (Waje). Burnley (Gida). Crystal Palace (Waje).

Wasanni 6 da suka rage wa City

Burnley (Waje). Eberton (Waje). Brentford (Gida). AFC Bournemouth (Waje). Crystal Palace (Gida). Aston Billa (Gida)

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
Wasanni

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.