ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Dama Ce Ta Ragewa Arsenal?

by Abba Ibrahim Wada
3 months ago
Arsenal

Masu sharhi a kwallon kafa suna ci gaba da bayyana ra’ayinsu a kan halin da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal take ciki na yiwuwar rasa gasar firimiya ta Ingila bayan da Arsenal din ta sake tsintar kanta a wani yanayi na rashin tabbas a karshen kakar wasa duk da cewa ana ganin har yanzu Arsenal din tana da damar lashe gasar.

Duk da cewa ana ganin Arsenal din ba za ta iya ba, amma har yanzu magoya bayan Arsenal na ci gaba da alhinin rashin nasarar da kungiyar ta yi a wasanta da Manchester City na ranar Lahadi. Rashin nasarar da kungiyar ta yi da ci 2-1 ya sake jefa ta cikin babbar barazanar gaza lashe Kofin Premier da ta shafe fiye da shekara 20 tana kishirwarsa.

A shekarun baya-bayan nan kungiyar kan nuna alamun lashe kofin ta hanyar hawa teburin gasar tare da bayar da tazara mai yawa, amma ana zuwa karshen kakar sai komai ya sukurkuce mata. Hakan ce ma ta sa masu bibiyar kwallon kafa, musamman masu hammaya da ita ke yi mata kirari da ”Kofi Haram”.

ADVERTISEMENT

A wannan kaka kungiyar ta yi yunkurin goge wannan kirari, musamman ganin yadda ta jima a kan teburin gasar ta tazara mai yawa da ta bai wa City ta biyu. To sai dai da alama da wuya hakar kungiyar ta cimma ruwa, bayan shan kaye da 2-1 a hannun AFC Bournemouth da kuma 2-1 a hannun City, lamarin da ya rage tazarar makin da ke tsakaninsu zuwa uku, yayin da Manchester City ta je ta doke kungiyar kwallon kafa ta Burnley a kwantan wasan da take da shi kuma ya ba ta damar komawa mataki na daya.

A yanzu da ya rage wasa biyar a karkare gasar tambayar da mafi yawan masu bibiyar kwallon kafa ke yi ita ce ko Arsenal za ta iya karya bakin kirarin da ake yi mata na Kofi Haram? ko kuwa dai tarihi zai ci gaba da maimaita kansa?

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

A wajen magoya bayan Arsenal, watan Afrilu ya ci gaba da kasancewa wata mafi tsanani a wajensu. Alkaluma sun nuna cewa a wannan watan ne Arteta ke yawan rashin nasara a wasannin Premier, wani abu da alamu ke nuna cewa zai maimaita kansa a wannan shekarar ma, kasancewar ta yi rashin nasara biyu zuwa yanzu a cikin watan.

Wasu suna ganin akwai rashin kwarewa a wajen mai horarwa Mikel Arteta musamman ta juriya da mayar da hankali saboda ana ganin ba za a hada shi da Pep Guardiola ba wanda shi ne ya koya wa Arteta aiki kuma ya zama mataimakinsa a Manchester City kafin daga baya Arsenal din ta dauki Arteta ya koma mai horar da ‘yanwasanta.

A watan Afrilun shekarar 2021, Arsenal karkashin Arteta ta yi wasa hudu, inda ta ci daya kawai, ta yi rashin nasara biyu tare da kunnen doki daya.

Haka ma a Afrilun shekara ta 2022, kungiyar ta buga wasa 5, ta ci biyu daga ciki ta kuma yi rashin nasara uku. A Afrilun shekara ta 2023 ma, Arsnela ta buga wasa 5, inda ta ci guda daya tare da yin kunnen doki a uku da kuma rashin nasara daya.

To amma a shekara ta 2024, abubuwa sun sauya, inda ta buga wasanni 6, ta ci 5 daga ciki da rashin nasara daya. Amma a Afrilun 2025 da ya gabata sai aka sake komawa gidan jiya, inda ta buga wasa 5, ta ci 2 da kunnen doki 3.Sai dai duk da haka Arteta na da kwarin gwiwa, kamar yadda ya bayyana a taron manema labarai da ya gabatar bayan wasan da suka yi rashin nasara a filin wasa na Ettihad.

Arteta ya ce sun yi rashin nasara a wasa mai muhimmanci, amma har yanzu suna da kwarin gwiwa kuma suna da yakinin cewa za su lashe gasar ta bana.

Wasanni 5 da suka rage wa Arsenal

Newcastle United (Gida). Fulham (Gida). West Ham United (Waje). Burnley (Gida). Crystal Palace (Waje).

Wasanni 6 da suka rage wa City

Burnley (Waje). Eberton (Waje). Brentford (Gida). AFC Bournemouth (Waje). Crystal Palace (Gida). Aston Billa (Gida)

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

An Kaddamar Da Ginin Tashar Ruwa Ta Kiwon Kifi Bisa Tallafin Sin A Saliyo

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.