ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Alireza Aarafi, Shugaban Kwamitin Zaɓen Sabon Ayatollah A Iran?

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Alireza

Hukumomin Iran sun sanar da Alireza Aarafi, wanda wakili ne a Majalisar Magabatan ƙasar, domin ya jagoranci majalisar tafiyar da mulkin riƙon-ƙwarya na ƙasar.

Bayan tabbatar da rasuwar Ali Khamenei a ranar 29 ga watan Fabarairu, za a kafa majalisar riƙon ƙwarya ta ƙasar, bisa dogaro da sashe na 111 na kundin tsarin mulkin ƙasar, wadda za ta ƙunshi shugaban ƙasa da babban alƙalin alƙalai da kuma wani wakili daga Majalisar Magabatan ƙasar.

  • Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas
  • Dalilin Da Ya Sa Muka Kai Wa Iran Hari — Donald Trump 

Bayan sanar da Mista Aarafi a matsayin mamban wannan majalisa, ana sa ran mutanen uku ne za su karɓi ragamar tafiyar da lamurran ƙasar har sai majalisar masana ta ƙasar ta sanar da sabon jagoran addinin ƙasar.

ADVERTISEMENT

Sashe na 111 na kundin tsarin mulki ya bayyana cewa, daga lokacin rasuwar jagoran addini zuwa lokacin da Majalisar Masana za ta sanar da sabon Jagora, Majalisar wasu mutane guda uku ne za su tafiyar da ayyukan ofishin Jagora.

Wakilan wannan majalisa su ne Shugaban ƙasa, da Babban alƙalin ƙasa da kuma wakilin Majalisar Magabata wanda Majalisar lura da buƙatun gaggawa ke zaɓa.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sai dai, wannan Majalisa ta Mutane uku ba ta da cikakken iko, kuma tana buƙatar amincewar kashi uku cikin huɗu na Majalisar lura da buƙatun gaggawa kafin aiwatar da abubuwa kamar haka:

Kasancewar an kashe babban kwamandan rundunar juyin juya halin ƙasar, da shugaban rundunar tsaro ta ƙasar da kuma da dama daga cikin manyan hafsoshin sojin ƙasar, ana sa ran majalisar shugabancin ta riƙon ƙwarya za ta riƙa zartar da manufofi ne ta hanyar samun amincewar kashi uku bisa huɗu na wakilan majalisar ƙasar.

Wasu kafofin yaɗa labarai na ciki da wajen ƙasar, ciki har da jaridar New York Times cewa an samar da “mataki huɗu na magadan jagororin” ƙasar, sai dai kafofin yaɗa labarai da ke kusa da gwamnatin ƙasar sun bayyana lamarin a matsayin “farfagandar yaƙi.”

Wane ne Alireza Aarafi?

Bayanai daga kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an haifi Alireza Aarafi ne a shekara ta 1955 a birnin Meybod da ke lardin Yazd.

Mahaifinsa Mohammad Ebrahim Aarafi shahararren malami ne a lokacin rayuwarsa, wanda ya yi adawa da jagorancin sarki Pahlaɓi, kuma yana da alaƙa ta ƙut da ƙut da malaman da ke kusa da Ruhollah Khomeini.

Mahaifiyarsa ‘ya ce ga Sheikh Kazem Malek Afzal Ardakani.

Alireza Aarafi ya yi karatunsa na farko-farko ne, kamar ilimin Ƙur’ani da adabi da harkar shari’a a wurin mahaifinsa da kuma wasu malamai.

Ya koma birnin Ƙom a shekarar 1960, sannan bayan kammala karatun elemantare ya fara karatun koyon maluntan addini a shekarar 1977.

Bayan kammala matakin farko, sai ya fara tafiya wurin manyan malaman shi’a daban-daban ya yi karatun shari’a, ciki har da Morteza Haeri, da Mohammad Fazel Lankarani, da Hossein Ɓahid Khorasani, da Jaɓad Tabrizi, da Ali Meshkini, da kuma Hassan Hassanzadeh Amoli, sannan ya yi karatun falsafa a wurin Mohammad Taƙi Misbah Yazdi.

Ya kuma yi karatun harkokin addini a tsangayoyi da jami’o’i kamar Allameh Tabataba’i da Tarbiat Modarres.

Alireza Aarafi ya kasance cikin harkokin siyasa tun yana matashi, kuma ya bi sahun mahaifinsa wajen adawa da gwamnatin Pahlaɓi.

An kama shi tare da ɗaure shi a gidan yari tun yana da shekara 16.

A shekarar 1979, an kafa wata ƙungiyar mai lura da ɗalibai waɗanda ba ƴan asalin ƙasar Iran ba a cibiyar karatun addini ta Ƙom.

Wadda daga baya ƙungiyar ta zama ‘Cibiyar Kimiyyar Musulunci ta Duniya’, inda ta koma ƙarƙashin kulawar jagoran addini na Iran.

A shekara ta 2002 ne aka naɗa Alireza Aarafi a matsayin shugaban cibiyar bisa amincewar Ayatollah Ali Khamenei.

Yana daga cikin iyayen jami’ar Kimiyyar Ƙur’ani da ilimi.

Aarafi ya kasance limamin Juma’a na Meybod tun daga shekara ta 1992, kuma an naɗa shi limamin juma’a na Ƙom a 1994.

Shi mamba ne a ƙungiyar malaman cibiyar horar da malaman addini ta Ƙom.

Mista Aarafi ya yi takarar shiga majalisar ƙwararru ta Iran a zaɓen shekara ta 2015 domin wakiltar mazaɓar Tehran, sai dai bai samu nasara ba.

Ya sake gwada yin takara a zaɓukan tsakiyar zango, inda ya samu nasara, domin wakiltar Tehran.

Ya samu shiga majalisar ne karon farko daga Tehran a zaɓen da aka yi a watan Maris na 2023, inda ya samu ƙuri’a 888,618.

A ranar 14 ga watan Yulin 2019 aka naɗa Mista Aarafi zuwa Majalisar Magabata bisa amincewar Ali Khamenei.

Daga Majalisar Masana zuwa jagoran riƙo

A shekarun baya-bayan nan ne mutane suka fara sanin Alireza Aarafi, a baya idan za a ambace shi a labarai, akan kira shi da laƙabin “Hujjat al-Islam”, amma a yanzu za a riƙa masa laƙabi da “Ayatollah”.

Alireza na cikin mutanen da Ali Khamenei ya amince da su kuma yana cikin na kusa da shi. Wannan karɓuwa da ya samu a wurin jagoran addinin ta sanya darajarsa ta riƙa ɗagawa, har ya kai ga inda ake ambaton sunansa a matsayin wanda zai iya gadon Ali Khamenei.

Alireza
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Rundunar Ƴansandan Nijeriya Ta Naɗa Sabon Kakaki

Rundunar Ƴansandan Nijeriya Ta Naɗa Sabon Kakaki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.