ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Tsoho Shekara Saba’in Ya Rasa Ransa A Rikicin Nadin Sarauta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Wani mutum dan shekara saba’in a duniya, Apollos Danlami ya rasa ransa yayin da wani kuma mai suna Naemiya Bature mai shekara 65 da wasu adadin mutane suka jikkata a wani rikicin da ya samo asali kan nadin sarautar Hakimin kauyen Sang da ke cikin karamar hukumar Bogoro a jihar Bauchi.

 

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi ta cikin sanarwar da ta fitar, inda ta ce, an fara samun rashin jituwar ne sakamakon boren da wasu fusatattun matasa suka yi na kin amincewa da nadin sarautar.

ADVERTISEMENT
  • Batun Leken Asiri Ya Shaida Manufar Kama Karya Ta Kasar Amurka

Sanarwar mai dauke da sanya hannun jami’in watsa labarai na hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil, ta ce, a sakamakon rikicin, fusatattun matasan sun banka wa gidaje 64 wuta, kona babura 3, da kadarorin miliyoyin naira sakamakon rikicin.

 

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sanarwar ta ce, “A ranar 15/04/2023 rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu rahoton cewa wani rikici na faruwa a yankin Bogoro. Binciken farko-farko ya nuna cewa rikici ne ya kunno kai a kauyen Sang da ke karamar hukumar Bogoro wanda ya samu asali daga batun nadin sarautar Hakimin Sang.”

Bauchi

Ahmad Wakil ya ce, wasu fusatattun matasa sun fito sun nuna adawarsu da nadin lamarin da ya kai ga juyawa zuwa rikici da har ya janyo mutuwa da jikkata wasu.

 

Wakil ya kara da cewa a kokarinsu na daukan matakin gaggawa domin shawo kan rikicin da daidaito da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, nan take rundunar ta tura karin jami’an ‘yansanda zuwa yankin domin tabbatar da zaman lafiya.

 

Sanarwar ta kara da cewa zuwa yanzu dai zaman lafiya ya farfado a yankin kuma dukkanin matakan kariya na tsaro an dauka.

 

Kan hakan Wakil ne ya sanar da cewa, hukumar na shirye wajen tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a a kowani lokaci, “Kuma ana cigaba da sintiri a yankin domin tabbatar da wani rikicin bai sake barkewa ba.”

 

Sanarwar ta nakalto cewa, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya umarci babban jami’in dan sanda a Bogoro da ya kaddamar da bincike domin gano hakikanin abubuwan da suka faru da suka janyo rikicin.

 

Kazalika, ya kuma ce, dukkanin kokari ya kankama wajen ganin an cafko tare da taso keyar wadanda ke da hannu a janyo wannan rikicin, inda ya ce da zarar aka kamo su to za a gurfanar da su a gaban kotu domin su dandana kudarsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.