ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Tsoho Shekara Saba’in Ya Rasa Ransa A Rikicin Nadin Sarauta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Wani mutum dan shekara saba’in a duniya, Apollos Danlami ya rasa ransa yayin da wani kuma mai suna Naemiya Bature mai shekara 65 da wasu adadin mutane suka jikkata a wani rikicin da ya samo asali kan nadin sarautar Hakimin kauyen Sang da ke cikin karamar hukumar Bogoro a jihar Bauchi.

 

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi ta cikin sanarwar da ta fitar, inda ta ce, an fara samun rashin jituwar ne sakamakon boren da wasu fusatattun matasa suka yi na kin amincewa da nadin sarautar.

ADVERTISEMENT
  • Batun Leken Asiri Ya Shaida Manufar Kama Karya Ta Kasar Amurka

Sanarwar mai dauke da sanya hannun jami’in watsa labarai na hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil, ta ce, a sakamakon rikicin, fusatattun matasan sun banka wa gidaje 64 wuta, kona babura 3, da kadarorin miliyoyin naira sakamakon rikicin.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Sanarwar ta ce, “A ranar 15/04/2023 rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu rahoton cewa wani rikici na faruwa a yankin Bogoro. Binciken farko-farko ya nuna cewa rikici ne ya kunno kai a kauyen Sang da ke karamar hukumar Bogoro wanda ya samu asali daga batun nadin sarautar Hakimin Sang.”

Bauchi

Ahmad Wakil ya ce, wasu fusatattun matasa sun fito sun nuna adawarsu da nadin lamarin da ya kai ga juyawa zuwa rikici da har ya janyo mutuwa da jikkata wasu.

 

Wakil ya kara da cewa a kokarinsu na daukan matakin gaggawa domin shawo kan rikicin da daidaito da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, nan take rundunar ta tura karin jami’an ‘yansanda zuwa yankin domin tabbatar da zaman lafiya.

 

Sanarwar ta kara da cewa zuwa yanzu dai zaman lafiya ya farfado a yankin kuma dukkanin matakan kariya na tsaro an dauka.

 

Kan hakan Wakil ne ya sanar da cewa, hukumar na shirye wajen tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a a kowani lokaci, “Kuma ana cigaba da sintiri a yankin domin tabbatar da wani rikicin bai sake barkewa ba.”

 

Sanarwar ta nakalto cewa, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya umarci babban jami’in dan sanda a Bogoro da ya kaddamar da bincike domin gano hakikanin abubuwan da suka faru da suka janyo rikicin.

 

Kazalika, ya kuma ce, dukkanin kokari ya kankama wajen ganin an cafko tare da taso keyar wadanda ke da hannu a janyo wannan rikicin, inda ya ce da zarar aka kamo su to za a gurfanar da su a gaban kotu domin su dandana kudarsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.