ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Tsoho Shekara Saba’in Ya Rasa Ransa A Rikicin Nadin Sarauta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Wani mutum dan shekara saba’in a duniya, Apollos Danlami ya rasa ransa yayin da wani kuma mai suna Naemiya Bature mai shekara 65 da wasu adadin mutane suka jikkata a wani rikicin da ya samo asali kan nadin sarautar Hakimin kauyen Sang da ke cikin karamar hukumar Bogoro a jihar Bauchi.

 

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi ta cikin sanarwar da ta fitar, inda ta ce, an fara samun rashin jituwar ne sakamakon boren da wasu fusatattun matasa suka yi na kin amincewa da nadin sarautar.

ADVERTISEMENT
  • Batun Leken Asiri Ya Shaida Manufar Kama Karya Ta Kasar Amurka

Sanarwar mai dauke da sanya hannun jami’in watsa labarai na hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil, ta ce, a sakamakon rikicin, fusatattun matasan sun banka wa gidaje 64 wuta, kona babura 3, da kadarorin miliyoyin naira sakamakon rikicin.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sanarwar ta ce, “A ranar 15/04/2023 rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu rahoton cewa wani rikici na faruwa a yankin Bogoro. Binciken farko-farko ya nuna cewa rikici ne ya kunno kai a kauyen Sang da ke karamar hukumar Bogoro wanda ya samu asali daga batun nadin sarautar Hakimin Sang.”

Bauchi

Ahmad Wakil ya ce, wasu fusatattun matasa sun fito sun nuna adawarsu da nadin lamarin da ya kai ga juyawa zuwa rikici da har ya janyo mutuwa da jikkata wasu.

 

Wakil ya kara da cewa a kokarinsu na daukan matakin gaggawa domin shawo kan rikicin da daidaito da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, nan take rundunar ta tura karin jami’an ‘yansanda zuwa yankin domin tabbatar da zaman lafiya.

 

Sanarwar ta kara da cewa zuwa yanzu dai zaman lafiya ya farfado a yankin kuma dukkanin matakan kariya na tsaro an dauka.

 

Kan hakan Wakil ne ya sanar da cewa, hukumar na shirye wajen tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a a kowani lokaci, “Kuma ana cigaba da sintiri a yankin domin tabbatar da wani rikicin bai sake barkewa ba.”

 

Sanarwar ta nakalto cewa, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya umarci babban jami’in dan sanda a Bogoro da ya kaddamar da bincike domin gano hakikanin abubuwan da suka faru da suka janyo rikicin.

 

Kazalika, ya kuma ce, dukkanin kokari ya kankama wajen ganin an cafko tare da taso keyar wadanda ke da hannu a janyo wannan rikicin, inda ya ce da zarar aka kamo su to za a gurfanar da su a gaban kotu domin su dandana kudarsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
Labarai

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
Labarai

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC
Labarai

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Next Post
Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.