ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Tsoho Shekara Saba’in Ya Rasa Ransa A Rikicin Nadin Sarauta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Wani mutum dan shekara saba’in a duniya, Apollos Danlami ya rasa ransa yayin da wani kuma mai suna Naemiya Bature mai shekara 65 da wasu adadin mutane suka jikkata a wani rikicin da ya samo asali kan nadin sarautar Hakimin kauyen Sang da ke cikin karamar hukumar Bogoro a jihar Bauchi.

 

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi ta cikin sanarwar da ta fitar, inda ta ce, an fara samun rashin jituwar ne sakamakon boren da wasu fusatattun matasa suka yi na kin amincewa da nadin sarautar.

ADVERTISEMENT
  • Batun Leken Asiri Ya Shaida Manufar Kama Karya Ta Kasar Amurka

Sanarwar mai dauke da sanya hannun jami’in watsa labarai na hukumar, SP Ahmed Mohammed Wakil, ta ce, a sakamakon rikicin, fusatattun matasan sun banka wa gidaje 64 wuta, kona babura 3, da kadarorin miliyoyin naira sakamakon rikicin.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Sanarwar ta ce, “A ranar 15/04/2023 rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu rahoton cewa wani rikici na faruwa a yankin Bogoro. Binciken farko-farko ya nuna cewa rikici ne ya kunno kai a kauyen Sang da ke karamar hukumar Bogoro wanda ya samu asali daga batun nadin sarautar Hakimin Sang.”

Bauchi

Ahmad Wakil ya ce, wasu fusatattun matasa sun fito sun nuna adawarsu da nadin lamarin da ya kai ga juyawa zuwa rikici da har ya janyo mutuwa da jikkata wasu.

 

Wakil ya kara da cewa a kokarinsu na daukan matakin gaggawa domin shawo kan rikicin da daidaito da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, nan take rundunar ta tura karin jami’an ‘yansanda zuwa yankin domin tabbatar da zaman lafiya.

 

Sanarwar ta kara da cewa zuwa yanzu dai zaman lafiya ya farfado a yankin kuma dukkanin matakan kariya na tsaro an dauka.

 

Kan hakan Wakil ne ya sanar da cewa, hukumar na shirye wajen tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a a kowani lokaci, “Kuma ana cigaba da sintiri a yankin domin tabbatar da wani rikicin bai sake barkewa ba.”

 

Sanarwar ta nakalto cewa, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya umarci babban jami’in dan sanda a Bogoro da ya kaddamar da bincike domin gano hakikanin abubuwan da suka faru da suka janyo rikicin.

 

Kazalika, ya kuma ce, dukkanin kokari ya kankama wajen ganin an cafko tare da taso keyar wadanda ke da hannu a janyo wannan rikicin, inda ya ce da zarar aka kamo su to za a gurfanar da su a gaban kotu domin su dandana kudarsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

Zaben Adamawa: INEC Ta Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Kwamishinanta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.