ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Gwamnonin Da Ake Hasashen Ba Za Su Koma Kan Kujerunsu Ba A 2027

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
2027

‘Yan siyasan Nijeriya sun fara muhawara kan zaben 2027, inda kowannensu ke aiki tukuru don tsare mukamansu a nan gaba. Sai dai kuma wasu gwamnonin da ke kan wa’adinsu na farko na iya yin rashin nasara a cikin zaben 2027.

Hakan zai ya faru ne saboda da yawa daga cikin gwamnonin da suka fara mulki a shekararsu ta farko sun fara ne da fadace-fadace maimakon gina kawance da habaka tsare-tsarensu na harkokin siyasa.

  • Pep Guardiola Ya Tsawaita Kwantiragi A Manchester City Har Zuwa Shekarar 2027
  • Shugaban Kasa: ACF Za Ta Goyi Bayan Ɗan Takarar Arewa A Zaɓen 2027

Wasu daga cikin fadace-fadacen da gwamnonin ke fafatawa suna da tasiri wajen tabbatar da sakamakon zabe a jiharsu.

ADVERTISEMENT

Binciken da aka yi a tsanake ya nuna cewa wasu gwamnonin sun fara shekara ta farko a kan karagar mulki suna yakar ubanningidansu na siyasa ba tare da wani tsarin siyasar da zai taimaka masu wajen komawa kan mulki ba, yayin da wasu ke yakar sarakunan masu daraja ta daya, wanda a karshe suna iya harzuka jama’a su juya musa baya.

Wasu daga cikin gwamnonin da ke hasashen ba za su dawo kan mukamansu ba sun hada da Gwamnan Sakkwato, Ahmad Aliyu Sokoto, Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara, Gwamnan Kaduna, Uba Sani, Gwamnan Benuwai, Hyacinth Alia, da kuma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, kadan Kenan daga ciki.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Dalilan da ya sa wadannan gwamnonin da aka ambata ake hasashen ba za su koma kan mukamansu ba saboda:

 

Gwamnan Sakkwato, Ahmad Aliyu

Gwamnan Jihar Sakkwato na daya daga cikin gwamnonin da suke cikin wa’adi na farko a Nijeriya, wanda ake hasashen ba zai iya yin nasara a 2027 ba idan har ya yi yunkurin tsayawa takara karo na biyu. Tun kafin ya cika shekara daya a kan karagar mulki, gwamnan ya sauke wasu sarakuna kusan 15 a jihar, bisa wasu laifuka daban-daban, lamarin da ka iya janyo masa cikas a burinsa na zarcewa a kan karagar mukli karo na biyu.

Bayan ‘yan watanni ne, kungiyar kare hakkin musulmi (MURIC) ta yi korafin cewa gwamnan na shirin tsige Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar. Ko da yake gwamnatin ta musanta wannan zargi, wanda kudirin a majalisar dokokin jihar ya tsallake karatu na biyu.

Idan kudirin zama doka, za a tsige Sarkin Musulmi daga wasu mukamai da suka hada da nadin sarakuna da hakimai, ba tare da sa hannun gwamna ba. Duk da cewa ana iya daukar wannan matakin a matsayin tsarin mulki saboda dokokin da aka yi amfani da su, zai iya jawo wa gwamna asarar wa’adin mulki na biyu domin Jihar Sakkwato da kuma matsayin Sarkin Musulmi na da alaka da addini.

Jaridar Punch ta kuma ruwaito cewa wata majiyar siyasa a jihar ta bayyana cewa gwamnan da magoya bayansa ba su taba boye tunanin tsige Sarkin Musulmi daga yakin neman zabensu ba. Majiyar ta bayyana cewa jam’iyyar APC mai mulki ta yi yakin neman zabe tare da bayyana cewa, ‘sabuwar gwamnati, sabon sarki’.

 

Gwaman Ribas, Siminalayi Fubara

Gwamna Jihar Ribas, Fubara yana daya daga cikin gwamnoni sahu na farko da ake hasashen ba za su iya sake lashe zabe 2027, saboda rashin jituwar da ke tsakaninsa da ubangidansa na siyasa, Nyesom Wike, wanda yanzu ya zama ministan babban birnin tarayya.

Rikicin Fubara da Wike ya samo asali ne watanni uku da fara mulkinsa a matsayin gwamnan Ribas, wanda da yawa daga cikin masu lura da harkokin siyasa tsammanin haka na iya faruwa ba a cikin karamin lokaci.

Amma Shugaban kasa, Bola Tinubu ya taba yi wa Wike alkawari a bainar jama’a cewa zai kyale shi wajen kaddamar duk wani aiki a Abuja. Don haka, tare da goyon bayan tarayya da na shugaban kasa, Wike na iya kayar da Fubara ko kuma ya kulla masa makircin tsige shi kafin karshen wa’adin mulkinsa ya kare.

Haka kuma, wani manazarci Okanlawon Gaffar, a wata tattaunawa ta musamman da ya yi da manema labarai, ya bayyana cewa Wike yana da kwarewa. A matsayinsa na tsohon gwamnan Jihar Ribas, ya san yadda zai yi nasara a matsayin ubangidan siyasa da kuma yadda za a iya kayar da wani a fagen harkokin siyasa.

Wani abin da bai kamata a manta da shi ba shi ne, hazakar Wike a siyasa. Ya fara siyasa ne tun a shekarar 1999. Kasancewarsa a jam’iyyar PDP da kuma yadda ya rike mukamin minista a jam’iyyar APC wata shaida ce da ke nuna hazakarsa.

Ko da yake a kwanakin baya, Gwamna Fubara ya yi nuni da cewa zai fice daga PDP, yana mai cewa jam’iyyar ta gaza a wurinsa, amma a halin yanzu Wike na da karfin jam’iyyar PDP da APC a Ribas. Har yanzu dai babu tabbas ko Fubara yana da tsarin siyasa mai karfi da zai kafa jam’iyyarsa ta siyasa ko kuma ya shiga karamar jam’iyya da zai iya kayar da Wike a zabe.

 

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya kasance yana da cikin gwamnonin da ke kan wa’adinsu na farko, wanda ake ganin cewa yana da matukar wahala ya zarce zuwa wa’adi na biyu ta hanyar kuri’un jama’a idan har ba a gaggauta warware takaddamar da ke tattare da tsige Sarkin Kano ba.

Duk da cewa wanda ya gada kuma yanzu shi ne shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, ya sha suka a kan tsige Muhammadu Sanusi, ana zargin gwamnan da sake yin wani kuskuren da Ganduje ya yi.

A zuwa 2027, al’ummar jihar za su iya neman gwamnan da zai iya daidaita rikicin masarautun, musamman ma a yanzu da ake ganin dalilin da ya sa wasu gwamnonin suka koma tsige sarakunan gargajiya, musamman Sarkin Musulmi.

Gwamnan Kaduna, Uba Sani

Gwamna Uba Sani shi ma wani gwamna ne da ke cikin wa’adinsa na farko da a halin yanzu yana fada da ubangidansa, Malam Nasir el-Rufai, ta hanyar majalisar dokokin jihar. Ba kamar Fubara ba, Sani yana da kwarewar siyasa a matsayinsa na tsohon sanata kuma ga dukkan alamu yana da goyon bayan mafi yawan ‘yan majalisar jihar.

Sai dai ga dukkan alamu tsohon gwamnan jihar na da goyon bayan al’umma, kuma hakan na iya karuwa fiye da yadda ake tsammani.

Alamu na nuni da cewa el-Rufai ma zai yi kokarin wanke sunansa, matakin farko shi ne, ya maka majalisar dokokin jihar kara a gaban kotu kan rashin sauraron karar da ‘yan majalisar suka yi masa na cin hanci da rashawa na naira biliyan 432 da ake zargin gwamnatinsa ta wawure.

Idan har el-Rufai ya samu nasara a babbar kotun Jihar Kaduna, hakan zai kara kaimi wajen hana gwamnan samun nasara a jihar a karo na biyu.

 

Gwamana Benuwai, Hyacinth Alia

Gwamnan Jihar Benuwai, Hyacinth Alia, shi ma ba ana hasashen zai yi wuya ya koma kan kujerarsa a 2027 idan har ya kasa samun goyon bayan sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, wanda a halin yanzu shi ne ke kuwa da tsarin jam’iyyar a jihar.

Alia ba shi da kwarewar siyasa kafin fitowarsa a matsayin dan takarar gwamna a APC a zaben 2023. Ko da yake zai yi amfani da matsayinsa wajen gina gadoji da samar da kokarin gina siyasarsa kafin 2027, dole goyon baya da karfin siyasar Akume su yi tasiri.

2027
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Xi: Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Morocco Wajen Goyawa Muhimman Muradun Juna Baya

Xi: Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Morocco Wajen Goyawa Muhimman Muradun Juna Baya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.