ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Taron Cikar Hadiza Bala Usman Shekara 50 A Duniya

by Bello Hamza
5 months ago
Hadiza

A ranar Talata 13 ga watan Janairu 2026 ne ƴanuwa da abokan arziƙi suka taru a babban ɗakin taro na Hillton Hotel Abuja inda suka yi gangamin taya Hajiya Hadiza Bala Usman, mai bai wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Shawara a kan Manufofi da Tsare-tsare murna cika shekara 50 a duniya.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ne ya jagoranci taron, a ciklin jawabinsa ya bayyana Hadiza Bala Usman a matsayin wata jaruma kuma kallabi a tsakanin rawunna inda ya bayyana ta a matsayin wadda ta gudanar da aikinta na gwamnati da gaskiya da riƙon amana, ta kuma zama abar koyi ga dukkan mata musamman daga arewacin Nijeriya dama ƙasa baki ɗaya.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Switzerland Bisa Afkuwar Bala’in Gobara
  • Na Ɗauki Harkar Fim Tamkar Aikin Gwamnati — Maryam Usman

Ya ce, “tabbas Hadiza ta samar wa kanta gurbi a kundin tarihin gudanar da ayyuka a ƙasar nan, saboda yawancin manyan ƙudurorin a gwamnatin nan ke aiwatarwa suna fitowa daga irin shwarwarin da ke fitowa daga ofishinta”

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma ce, “Hadiza Bala Usman ta samar wa kanta wannan sunan ne ta hanyar sadaukarwa, gaskiya da riƙon amana a dukkan wuraren da ta yi aiki” ya ce hakan abin a yaba ne musamman ganin daga ɓangaren ƙasar nan da ta fito inda mata basa samun cikkaken damar bayyana irin baiwa da basirar da Allah Ya basu.”

Ya kuma jaddada cewa, waɗannan nasarori da Hadiza ta samu ba bisa haɗari ba ne kuma ƴan Nijeriya na nan suna sa ido tare da fatan Allah ya cika mata dukkan burinta na alhairi, daga ƙarshe ya yi addu’ar Allah ya ƙara mata tsawon rai cikin ƙoshin lafiya da ƙaruwar arziƙi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Tun da farko, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya ce, tabbas Hadiza Bala Usman ta zama jagora kuma manuniya abar koyi ga dukkan matan Nijeriya. Ya kuma umarce ta da ta ci gaba da tsayuwa wajen kare ƙudurorin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ƙara da cewa, rayuwarta a nan gaba zai ƙara bayyana irin baiwar da Allah ya yi mata, ‘Za mu ci gaba da sa ido a kan irin gudummawar da “Za ki ci gaba bayarwa ga ƙasarmu Nijeriya”.

A nasa jawabin, Shugabhan Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Hon. Femi Gbajabiamila, ya bayyana cewa, an gudanar da taron ne domin jinjinawa ga irin gaggarumnin gudummwar da Hadiza bayar ga tattabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, gudummwa ne yawancin ƴan Nijeriya basu sani ba saboda yawancin gudummawar daga bayan fage take bayar da su, haka kuma ya ƙara wa tafiyar gwamnatin Tinubu mutumci da a idon al’ummar ƙasa dama na ƙasashen waje.

Gbajabiamila ya bayyana irin gaggarumin ayyuka da sake fasalin da ta gudanar a lokacin da take shugabantar Hukumar Jirage Ruwa ta Nijeriya (NPA), inda ta kasance mace ta farko data jagoranci hukumar. Ya ce tabbas a Nijeriya ba za a taɓa mantawa da irin ayyukan alhairin data gudanar ba inda ta farfaɗo da mutuncin hukumar a idon duniya.

Haka kuma a nashi jawabin, Ministan Ci Gaban Matasa, Ayodele Olawande, ya ce, Hadiza Bala Usman ta yi fice a ɓangaren samar da ci gaban mata da matasa, ana iya ganin haka ne musamman a irin yadda ta jagoranci fafutukar nemo ceto ƴan matan nan da aka sace a shekarun baya inda ta ƙirƙiro da tafiyar ‘BRING BACK OUR GIRLS’.

A jawabinta, Shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa NEMA, Hajiya Zubaida Umar Abubakar, ta bayyana Hadiza Usman a matsayin ƙawa wadda ta sani na tsawon fiye da shekara 30, ta ce a tsawon waɗannan shekarun ta santa ne a matsayin mai gaskiya da riƙaon amana tare da taimakon al’umma a duk inda ta samu kanta. “Wannan haka yake a rayuwarta na aikin gwamnati da rayuwarta na ƙashin kanta”.

Shugaban Hukumar Sauya Fasalin Ayyukan Gwamnati, Dr. Joe Abah ya gabatar da muƙala mai taken “Leadership Deliɓery and the Courage to Serɓe,” a wajen taron, inda bayyana cewa, yin aiki a matsayin bnabban ma’aikacin gwamnati a ƙasar nan a halin yanzu wani babban baiwa ce da ba kowa yake samu ba, a kan haka dole duk wanda ya samu wannan damar ya tabbatar da ya yi ayyukan da za su inganta rayuwar al’ummar ƙasa.

Ya bayyana cewa, a kwai manyan darussa a rayuwar Hadiza musamman a kan yadda ta gudanar da harkookin ayyukanta na gwamnati, “musamman a irin wannan lokacin ake yawo labaran ƙaryan kurege a faɗin ƙasar nan’.

Ya lura da cewa, harkar shugabanci na da matuƙar wahala, domin mutane basa iya ganin ƙoƙarinka har sai ka bar muƙamin da kake a kai amma ita Hadiza Bala Usman tun kafin ta bar muƙaman ta ake ganin irin yadda take bayar da gudummawa a ɓangarori da dama na rayuwar al’umma da kuma gudummwarta a wajen inganta ayyukan gwamnati.

A nata ɓangaren Hajiya Hadiza Bala Usman, ta bayyana jin daɗi da godiyarta ga Mataimakin Shugaban Ƙasa Sanata Kashim Shettima a kan yadda ya samu lokacin halartar taron taya murna duk da ɗimmbin ayyuykan da ke gabansa, ta kuma miƙa godiyarta ga Shugaba Tinubu da Mataimakinsa a kan yadda suka bata dama bayar da gudummwarta a wannan gwamnatin da kuma yadda ta samu damar bunƙasa rayuwarta.

Ta bayyana irin yadda ta bayar da gudummwa a shirye-shiryen tsara zaɓuɓaka tun a shekarar 2015 da kuma irin yadda ta gudanar da ayyukanta a lokacin da take shugabancin Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa NPA. Ta ce ta nan a kan aƙidarta na tabbatar da bunƙasa rayuwar al’umma musamman ta tsarin shugaba Tinubu na ‘Renewed Hope Agenda’

An dai haifi Hadiza Bala Usman ne a ranar 14 ga watan Janairu 1976 a garin Zariya ta Jihar Kaduna ga iyalan shaharren malamin tarin n nan na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya Dakta Bala Usman, inda ta samu horo na musamman na zama tsayayyiya mai gudanar da harkokinta cikin gaskiya da riƙon amana. A tsawon shekarun ta samu nasarar samun ci gaba a harkokin ayyuklan gwamanti ta kuma zama abar koyi ga mata na zamaninta.

Ta gina harkar karatunta ne daga Jami’ar Ahamdu Bello Zariya inda ta karanta harkokin gudanar da kasuwanci ‘Business Administration’ kafin ta wsuce Jami’ar ‘Uniɓersity of Leeds’ da ke Birtaniya inda ta samu babban digirinta a na ne ta ƙara samun ƙwarewar ɓangaren shugabanci da tafiyar dea al’umma.

Hadiza ta fara aikin gwamnati ne a hukumar (BPE) daga nan kuma ta zama mataimakiya ta mussamman ga Ministan Babban Birnin tarayya Abuja.sunan ta ya yi fice ne a shekarar 2014 a lokacin da suka ƙirƙiri gwagwamaryar neman ceto ƴan matan makarantar Chibok 200 da aka sace Bring Back Our Girls (BBOG). Inda tafiyar ya zama kafar isar da saƙo ga ƴanuwa da al’umma domin ganin an sako ƴan matan waɗanda ƙungiyar Boko Haramn suka sace.

A shekarar 2016, Hadiza Bala Usman ta kafa tarihi a yayin ta zama mace ta farko data riƙe muƙamin shugabar Hukumar Kula da Tashosin Jiragejn Ruwan Nijeriya (NPA), wanda ɓangare ne maza suka mamaye a shekarun baya. Za a ci gaba da tunawa da irin ayyukan alhairin da ta gabatar a NPA a  shekaru masu zuwa.

Hadiza
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Nemi A Hukunta Likitocin Da Suka Manta Da Almakashi A Cikin Wata Mata Da Ya Yi Sanadiyyar Mutuwarta

An Nemi A Hukunta Likitocin Da Suka Manta Da Almakashi A Cikin Wata Mata Da Ya Yi Sanadiyyar Mutuwarta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.