ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kashe Kanal Da Sojoji 7 A Sabon Harin Boko Haram

by Sani Anwar
2 months ago

Kwamandan Bataliya ta 242, da ke Monguno, Kanal I.A. Mohammed, da sojoji kusan aƙalla 10 ne suka rasa rayukansu a lokacin da wasu bama-bamai da ake kyautata zaton ƴan tada ƙayar baya ne suka dasa a Ƙaramar Hukumar Monguno ta Jihar Borno.

Majiyoyin cikin gida sun ce, an kashe Kanal Mohammed, a lokacin da yake wani aikin ƙarfafa gwiwa, bayan wani harin da aka kai da daddare a sansanin sojoji. An ce, lamarin ya faru ne a lokacin da jami’in sojan ya amsa kiran gaggawa daga sojojin da aka kai wa hari a wani sansanin sojoji na ‘Forward Operating Base’ (FOB), da ke da alaƙa da bataliya ta 242.

  • Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
  • Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
  • An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

A cewar majiyoyin, motarsa ta afka cikin bam ɗin ne a lokacin da yake gaggawar taimaka wa sansanin sojoji na FOB, bayan da wasu da ake zargin ƴan ta’adda ne suka ƙaddamar da farmakin haɗin gwiwa a daren Lahadi.

ADVERTISEMENT

Daily trust ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne kwana uku kacal bayan da wani Kwamandan runduna ta 29, Birgediya Janar Oseini Braimah tare da wasu sojoji aƙalla 17 ake zargin ƴan ta’addan da kashe su, a yayin harin da rundunar ta kai a Benisheikh da ke Ƙaramar Hukumar Kaga ta Jihar Borno.

Jami’in yaɗa labarai na rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, ‘Operation HADIN KAI’, Laftanar Kanar Sani Uba, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce; lamarin ya faru ne a yammacin ranar 12 ga watan Afrilu, lokacin da dakarun sashen 3 na OPHK, suka kai wa wani harin ta’addancin Tango saniyar ware a cibiyar Charlie 13 a Monguno.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

A cewarsa, bayan musayar wuta mai tsanani, sun fatattaki ƴan ta’addar tare da ci gaba da kula da wurin.

“Abin takaici, kwamandan rundunar, yayin da yake tafiya cikin ƙwarin gwiwa zuwa wurin da sojojin suke, domin tantance lamarin, ya ci karo da wata na’ura mai ɗauke da bama-bamai (IED), wacce ta yi wa motarsa mummunar illa, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa tare da wasu jami’an leƙen asiri guda shida.

Ya ce, ƙungiyar OPHK ta yi matuƙar alhinin rashin wannan babban jami’in da sauran jajirtattun ma’aikatan da suka sadaukar da rayuwarsu a hidimar ƙasa.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ” sadaukarwar da suka yi za ta kasance abar tunawa da sojojin da kuma al’ummar da suka yi wa hidimar.”

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Next Post
An Ƙirƙiro Da Shirin ‘Kano First’ Ne Don Sanya Wa Kanawa Kishin Jiharsu —Bala Gwagwarwa

An Ƙirƙiro Da Shirin 'Kano First' Ne Don Sanya Wa Kanawa Kishin Jiharsu —Bala Gwagwarwa

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.