Kwamandan Bataliya ta 242, da ke Monguno, Kanal I.A. Mohammed, da sojoji kusan aƙalla 10 ne suka rasa rayukansu a lokacin da wasu bama-bamai da ake kyautata zaton ƴan tada ƙayar baya ne suka dasa a Ƙaramar Hukumar Monguno ta Jihar Borno.
Majiyoyin cikin gida sun ce, an kashe Kanal Mohammed, a lokacin da yake wani aikin ƙarfafa gwiwa, bayan wani harin da aka kai da daddare a sansanin sojoji. An ce, lamarin ya faru ne a lokacin da jami’in sojan ya amsa kiran gaggawa daga sojojin da aka kai wa hari a wani sansanin sojoji na ‘Forward Operating Base’ (FOB), da ke da alaƙa da bataliya ta 242.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
A cewar majiyoyin, motarsa ta afka cikin bam ɗin ne a lokacin da yake gaggawar taimaka wa sansanin sojoji na FOB, bayan da wasu da ake zargin ƴan ta’adda ne suka ƙaddamar da farmakin haɗin gwiwa a daren Lahadi.
Daily trust ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne kwana uku kacal bayan da wani Kwamandan runduna ta 29, Birgediya Janar Oseini Braimah tare da wasu sojoji aƙalla 17 ake zargin ƴan ta’addan da kashe su, a yayin harin da rundunar ta kai a Benisheikh da ke Ƙaramar Hukumar Kaga ta Jihar Borno.
Jami’in yaɗa labarai na rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, ‘Operation HADIN KAI’, Laftanar Kanar Sani Uba, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce; lamarin ya faru ne a yammacin ranar 12 ga watan Afrilu, lokacin da dakarun sashen 3 na OPHK, suka kai wa wani harin ta’addancin Tango saniyar ware a cibiyar Charlie 13 a Monguno.
A cewarsa, bayan musayar wuta mai tsanani, sun fatattaki ƴan ta’addar tare da ci gaba da kula da wurin.
“Abin takaici, kwamandan rundunar, yayin da yake tafiya cikin ƙwarin gwiwa zuwa wurin da sojojin suke, domin tantance lamarin, ya ci karo da wata na’ura mai ɗauke da bama-bamai (IED), wacce ta yi wa motarsa mummunar illa, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa tare da wasu jami’an leƙen asiri guda shida.
Ya ce, ƙungiyar OPHK ta yi matuƙar alhinin rashin wannan babban jami’in da sauran jajirtattun ma’aikatan da suka sadaukar da rayuwarsu a hidimar ƙasa.
Sanarwar ta ƙara da cewa, ” sadaukarwar da suka yi za ta kasance abar tunawa da sojojin da kuma al’ummar da suka yi wa hidimar.”















Discussion about this post