Kwamandan Bataliya ta 242, da ke Monguno, Kanal I.A. Mohammed, da sojoji kusan aƙalla 10 ne suka rasa rayukansu a lokacin da wasu bama-bamai da ake kyautata zaton ƴan tada ƙayar baya ne suka dasa a Ƙaramar Hukumar Monguno ta Jihar Borno.
Majiyoyin cikin gida sun ce, an kashe Kanal Mohammed, a lokacin da yake wani aikin ƙarfafa gwiwa, bayan wani harin da aka kai da daddare a sansanin sojoji. An ce, lamarin ya faru ne a lokacin da jami’in sojan ya amsa kiran gaggawa daga sojojin da aka kai wa hari a wani sansanin sojoji na ‘Forward Operating Base’ (FOB), da ke da alaƙa da bataliya ta 242.
- An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
- Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
- Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
- Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
- Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
A cewar majiyoyin, motarsa ta afka cikin bam ɗin ne a lokacin da yake gaggawar taimaka wa sansanin sojoji na FOB, bayan da wasu da ake zargin ƴan ta’adda ne suka ƙaddamar da farmakin haɗin gwiwa a daren Lahadi.
Daily trust ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne kwana uku kacal bayan da wani Kwamandan runduna ta 29, Birgediya Janar Oseini Braimah tare da wasu sojoji aƙalla 17 ake zargin ƴan ta’addan da kashe su, a yayin harin da rundunar ta kai a Benisheikh da ke Ƙaramar Hukumar Kaga ta Jihar Borno.
Jami’in yaɗa labarai na rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, ‘Operation HADIN KAI’, Laftanar Kanar Sani Uba, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce; lamarin ya faru ne a yammacin ranar 12 ga watan Afrilu, lokacin da dakarun sashen 3 na OPHK, suka kai wa wani harin ta’addancin Tango saniyar ware a cibiyar Charlie 13 a Monguno.
A cewarsa, bayan musayar wuta mai tsanani, sun fatattaki ƴan ta’addar tare da ci gaba da kula da wurin.
“Abin takaici, kwamandan rundunar, yayin da yake tafiya cikin ƙwarin gwiwa zuwa wurin da sojojin suke, domin tantance lamarin, ya ci karo da wata na’ura mai ɗauke da bama-bamai (IED), wacce ta yi wa motarsa mummunar illa, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa tare da wasu jami’an leƙen asiri guda shida.
Ya ce, ƙungiyar OPHK ta yi matuƙar alhinin rashin wannan babban jami’in da sauran jajirtattun ma’aikatan da suka sadaukar da rayuwarsu a hidimar ƙasa.
Sanarwar ta ƙara da cewa, ” sadaukarwar da suka yi za ta kasance abar tunawa da sojojin da kuma al’ummar da suka yi wa hidimar.”















Discussion about this post