ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 months ago
Azumi

Kamar yadda muka yi bayani a baya, azumin watan Ramadana wajibi ne ga dukkan Musulmi baligi mai lafiya, ba mara lafiya ba. Wajibcin azumi kamar yadda Allah ya fada a cikin Alƙur’ani da fadarsa yana cewa:

“Ya ku Muminai, Allah Ya wajabta muku yin azumi kamar yadda Ya wajabta ma waɗanda suka zo kafin ku, ko za ku ji tsoron Ubangijinku. Kwanaki ne ƙididdigaggu. Wanda ya kasance a cikinku bai da lafiya ko kuma yana kan tafiya, to ya rama abin da ya kubuce masa a wasu ranakun. Waɗanda kuma ba za su iya yin azumin ba, to su ciyar da miskinai. Amma wanda yake da damar ciyar da miskinai da yawa, to ya yi alkhairi ne a wajensa. Lallai yin azumin ya fi alkhairi a gare ku, idan kun san alkhairin da ke cikinsa.

Lallai watan Ramadana da aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane, sannan kuma akwai ayoyi bayyanannu a cikinsa masu shiryarwa zuwa ga Allah da bayyana hukunce-hukunce. Duk wanda ya halarci ganin watan, to ya azumce shi. Wanda kuma bai da lafiya ko kuma yana kan tafiya, to ya biya abin da ya tsere masa a sauran wasu ranakun. Allah sauƙi yake nema daga wurinku, ba wahalarwa ba. Allah yana son ku cika adadin azumin, sannan yana son ku yi masa kirari daga abin da Ya shiryar da ku, ko za ku gode masa?”

ADVERTISEMENT

Yana daga cikin falalar azumi cewa yana sa tsoron Allah, saboda yana karya sha’awa. Yana daga cikin fa’idar azumi, Allah ya ce don mu yi takawa. Takawa mataki-mataki ce: akwai ta gama-gari, da ta kebantattu, da ta kebantattun kebantattu.

Takawa ta gama-gari: ita ce a bar ci da sha har izuwa faɗuwar rana, sannan a yi aiki don neman lada, a kuma bar abin da bai dace ba. Wannan takawar ba ta hana wasu yin abin da bai dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Takawa ta kebantattu: ita ce a bar ci da sha har izuwa faɗuwar rana, a yi ayyuka don Allah, sannan ba za su yi ƙarya ba, ba za su yi husuma ba, ba za su yi cece-kuce ba. Za su shiga cikin ibada ta ko’ina.

Takawa ta kebantattun kebantattu: sun haɗa duk abin alkhairi na gama-gari, sun haɗa duk abin alkhairi na kebantattu, sannan sun ƙara da nutso da zurfafawa cikin sanin Allah. Ba su ganin wani sai Allah; a ko da yaushe suna fadar Allah ko fadar Annabi (SAW) ko fadar waliyyan Allah.

Waɗannan takawa guda uku, Allah ya faɗa mana su cikin Alƙur’ani yana cewa:

“Ba laifi ga waɗanda suka yi imani da Allah suka yi aiki mai kyau cikin abin da suka ci, idan suka yi takawa suka yi imani, sannan suka yi wata takawa kuma suka yi imani, sannan suka yi wata takawa sannan suka yi kyautaye.”

Ayar ta sauka ne lokacin da ayar haramta giya ta sauka, sai wasu daga cikin muminai suka shiga shakku suna cewa: “To yanzun ‘yan uwanmu muminai da suka sha giya a baya kuma suka mutu fa?” Sai Allah ya saukar da wannan ayar yana mai cewa ba laifi a gare su, domin sun mutu lokacin da ba a haramta giya ba.

Alhamdulillah, duk waɗannan takawa guda uku suna daga cikin falalar Ramadana: takawa cikin Musulunci, takawa cikin Imani, sai takawa cikin Ihsani.

Azumin Ramadana kwanaki ne ƙididdigaggu, wata ɗaya ne kacal cikin watanni sha biyu. Allah ya bayyana mana cewa Ya san akwai marasa lafiya a cikinmu kuma akwai matafiya, don haka su ƙididdige kwanakin da azumi ya tsere musu su rama a wasu kwanakin.

Ayar da ta gabata ta bayyana wajibcin azumin watan Ramadana a Alƙur’ani, sai kuma hadisi mai zuwa ya tabbatar da wajibcin azumin a Sunnah ta Annabi (SAW):

“An gina Musulunci a kan shika-shikai guda biyar:

Shaidawa babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad (SAW) Manzon Allah ne.

Tsayar da sallah.

Ba da zakka.

Azumin watan Ramadana.

Ziyartar Dakin Allah mai girma.”

Ya zo a cikin hadisin Dalhatu bin Abdullahi cewa wani mutum ya tambayi Annabi (SAW): “Ya Manzon Allah, gaya min abin da Allah ya wajabta min na azumi.” Sai Annabi ya ce: “Watan Ramadana.” Sai mutumin ya ce: “Akwai wani kuma?” Sai Annabi ya ce: “A’a, sai dai idan za ka yi na nafila.”

Babu jayayya a cikin al’ummar Musulmi kan wajibcin azumin watan Ramadana.

An wajabta azumin watan Ramadana ranar Litinin, bayan hijira shekara ta biyu. Bayan Annabi (SAW) ya yi hijira zuwa Madina, a cikin shekara ta biyu ne aka wajabta azumi.

Alhamdulillah, abin da ya gabata shi ne bayanin azumi daga littafin Allah, da Sunnah ta Annabi Muhammad (SAW), da kuma haɗin kan al’ummar Musulmi kan wajibcin azumi.

Nasa’i ya ruwaito daga Abi Umamata cewa ya ce: “Ya Manzon Allah, horar da ni da wani aiki.” Sai Manzon Allah (SAW) ya ce: “Na hore ka da yin azumi, bayan farillah ka dinga yin nafila, domin azumi ba shi da kama cikin ibada.” Domin kowace ibada riya na iya shiga, amma azumi ba haka ba ne.

Wannan ya nuna alaƙar Ubangiji da azumi, domin Ubangiji ba shi da misali kamar yadda azumi ma ba shi da misali.

Muslim ya ruwaito daga Abi Huraira cewa Manzon Allah (SAW) ya ce:

“Ubangiji Ya ce dukkan ibadar ɗan Adam tasa ce, sai dai azumi nawa ne, kuma ni ne zan saka masa.”

Ya zo cikin hadisi cewa:

“Azumi garkuwa ne. Idan ɗayanku yana azumi, kada ya faɗi magana mara kyau, kada ya yi hayaniya. Idan wani ya zage shi ko ya nemi husuma da shi, ya ce ni mai azumi ne. Na rantse da wanda ran Annabi Muhammad (SAW) ke hannunsa, warin bakin mai azumi ya fi ƙamshi a wurin Allah ranar lahira fiye da turaren almiski.”

Muslim ya ruwaito daga Sa’adu cewa Manzon Allah (SAW) ya ce:

“A cikin Aljanna akwai wata ƙofa ana kiranta Rayyanu, ba masu shiga ta sai masu azumi.”

Mu sani ya ku ‘yan uwa, Allah Ya amsa mana azumin Ramadana. Ma’anar azumi ita ce kamewa. Azumi ibada ce da babu misalinta kamar yadda Ubangiji ba shi da misali. Kowace ibada ana cewa “na yi” — na yi sallah, na yi zakka amma azumi ana cewa “na bari”  na bar ci, na bar sha, na bar saduwa da iyali.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allah.

Alhamdu lillah.

Azumi
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
Siyasa

Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed

May 5, 2026
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
Addini

Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…

March 20, 2026
Next Post
Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

Matakin Soke Harajin Kwastam Ya Shaida Niyyar Kasar Sin Ta Taimakawa Kasashen Afirka A Kokarinsu Na Zamanantar Da Kansu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.