ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
NPA

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA ta alakanta rashin samar da daidaito a hada-ahadar kasuwanci. Ta alakanta hakan ne, musamman kan samun raguwar fitar da kaya zuwa ketare, masu yawa.

 

A cewarta, wannan kalubalen, ya kasance daya daga cikin manyan matsalolin da ya sanya, take cazar kudade da yawa a Tashohinta.

ADVERTISEMENT
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Masana’antun Nijeriya Sun Kashe Naira Tiriliyan 1.11 Wajen Samun Wutar Lantarki A 2024 – Rahoto

Shugabanta, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana haka a wajen taron da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Legas LCCI da kuma Kungiyar Masu Ruwa da Tsaki kan samar da inganci a Tashar Jiragen Ruwa suka shirya a Legas.

 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

“Rashin samar da daidaito a hada-ahadar kasuwanci, ya kasance abinda ya sanya Hukumar ta NPA ke cazar kudaden gudanar da aiki da yawa,” Inji Dantsoho.

 

Dantsoho wanda Janar Manaja na sashen hudda da jama’a da gudanar da tsare-tsare na Hukumar NPA Miista Seyi Iyawe Akinyemi ya wakilce shi a wajen taron, ya ce, NPA ta bai wa kamfanini biyar Lasisi a jihar Legas, bisa kokarin da take yi, na bunkasa fitar da kaya zuwa waje ta hanyar amfani da Tashoshin ta.

 

Sai dai, ya sanar da cewa, Hukumar na duba yuwuwar samar da rangwamen cazar kudaden, musamman domin ta kara inganta ayyukanta.

 

Ya yi nuni da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa waje ne da ke taimaka wa wajen kara habaka tattalin arzikin kasa, musamman saboda shigowar kasuwanci cikin kasar.

 

Dantsoho ya kara da cewa, yin ragin, zai bayar da dama wajen kara karfafa gasa a kasashen da ke Afiraka.

 

Shi ma a na sa sakon a wajen taron Babban Sakatare kuma Shugaban Majalisar Masu Fiton Kaya zuwa Ketare NSC, Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya sanar da cewa, tabbatar da inganci a Tashar Jiragen Ruwa, abu da ya wuce, batun jigar kaya a Tashar, amma ana da bukatar komi ya tafi yadda ya kamata.

 

Ukeyima, ya bayyana haka ne, ta bakin Madam Margaret Ogbonna, Daraktar Sashen Kula da Ayyuka a NSC, ya kara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, na fuslantar cazar kudade da yawa a yankin Afirka, musamman duba da yadda cazar kudaden, suka kai daga kashi 30 zuwa 40, wanda ya dara na Afirka ta Yamma.

 

A cewarsa, a yanzu, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, rashin inganci, wanda hakan ke ci gaba da shafar gudanar da hada-gadar kasuwanci.

 

Ya ci gaba da cewa, a yayin da Nijeriya ke ta kokarin tara sama da kashi 85 a cikin dari na fannin hada-hahadar kasuwancinta, musamman ta hanyar yin amfani da Tashoshin Jiragen Ruwanta, sai dai, cazar kudade da yawa a Tashohin Jiragen Ruwan Kasar, akalla a cikin kwana 18 zuwa 20, na ci gaba da zama kalubale, musamman duba da yadda cazar kudaden, daga kwana 3 uwa 5 suka dara na duniya.

 

“Wannan matsalar na janyo jinkiri da kuma shafar shiga da fitar da kaya.” Inji Ukeyima.

 

Ya bayyana cewa, domin a lalubo da mafita kan wannan matsalar, NSC ta mayar da hankali wajen ganin an wanzar da matakan da suka dace, musamman na bunkasa kundin farashi a Tashar Jiragen Ruwan Kasar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin na maraba, Shugaban LCCI, Mista Gabriel Idahosa, ya alakanta Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasar, a matsayin fannin da ke kara bunakasa gasar gudanar da hada-hadar kasuwanci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa.

 

“Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun kasance wata mahada ce ta gudanar da hada-hadar kasuwanci ta kasa da kasa, musamman duba da yadda ake fhigar da kaya da kuma fitar da su waje,” Inji Idahosa.

 

“Tabbabar da ingancin gudanar da ayyuka a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, ta hanyar rage cazar kudade masu yawa, tabbatar da ana tura kaya kan lokaci, karfafa gasar hada-hadar kasuwanci, na kara taimakawa Tashoshin,” A cewar Idahosa.

 

Ya kara da cewa, amma rashin tabbatar da ingancin, kara yawan cazar kudade, na rage yawan adadin hada-hadar kasuwancin da ake bukatar gudanar wa, wanda kuma hakan, ke janyo tattalin azriki nakasau.

 

A cewarsa, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, sun jima suna fuskanatar matsaloli, wanda hakan ya janyo rashin samar da inganci da kuma bayar da gudunmawarsu, kan habaka tattalin arzikin kasar.

 

“Daya daga cikin manyan kalubalen da Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ke fuskanta sun hada da samun cunkoso a Tashoshin da kuma samun jinkiri, musamman a Tashar Apapa da ta Tin Can Island da ke a jihar Legos, “ Inji Idahosa.

 

“Kayan aikin a Tashoshin, an jima ana yin amfani da su, wanda hakan ke haira da samun jinkirin gudanar da aiki, cazar kudade da yawa na tura kaya, wanda hakan ke sanya ba a samun damar gudanar da gasar hada-hadar kasuwanci, kamar yadda ta dace,” A cewar Idahosa.

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
NPA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri

Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.