ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Ganduje

Wani binciken jaridar Premium Times na musamman ya tona asirin irin yadda tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya janye hannun jihar daga kamfanin Dala Inland Dry Port Limited, inda ya mayar da hannun jarin jihar ga ƴaƴansa, kafin ya ba da kwangilar aikin gina kayayyakin more rayuwa a tashar akan biliyoyin Naira.

Binciken da aka yi ya nuna cewa, a shekarar 2020, Gwamna Ganduje ya yi wata yarjejeniya a asirce wadda ya musanya hannun jarin Kano na kashi 20 cikin 100 a kamfanin Dala Inland Dry Port, ya kuma sanya ƴaƴansa uku – Abdulaziz, Umar, da Muhammad Abdullahi Umar – a matsayin masu hannun jari kuma daraktocin kamfanin.

  • Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 
  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Yadda Aka Fara Maganar Hannun Jarin

ADVERTISEMENT

A shekarar 2006, lokacin mulkin Gwamna Ibrahim Shekarau, Jihar Kano ta sayi hannun jari na kashi 20% a kamfanin Dala Inland Dry Port. Yarjejeniyar ta tanadi cewa jihar za ta biya kuɗin hannun jarin ta ne ta hanyar gina ababen more rayuwa kamar hanyoyi, wutar lantarki, da samar da ruwa a wurin da ake ginawa a Zawachiki, Kano.

Sai dai, gwamnonin da suka gabace shi, Shekarau da Rabiu Kwankwaso, ba su yi wani aikin da yarjejeniyar ta tanada ba  na gina waɗannan kayayyakin ba. Wannan rashin aiki ya kai ga cewa Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Nijeriya (Nigerian Shippers’ Council) ta yi barazanar soke yarjejeniyar da kamfanin a shekarar 2019 saboda rashin cimma yarjejeniyar mallakar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Shigowar Ganduje Da Sauya Mallaka A Asirce

Sakamakon barazanar soke yarjejeniyar ya sa dole wanda ya kafa kamfanin, Ahmad Rabiu, ya nemi sabon abokin tarayya. A cikin wannan lokacin ne, a ranar 5 ga Maris, 2020, aka gudanar da wani taro na musamman na kamfanin Dala Inland Dry Port.

A cikin wannan taron, an cire duk tsoffin daraktocin kamfanin, an kuma naɗa ƴaƴan Ganduje uku da wani ɗan nasa na kut da kut mai suna Abubakar Bawuro, a matsayin sabbin daraktoci. An ba kowane ɗaya daga cikin ƴaƴan Ganduje hannun jari na kashi 20% kowanne, haka kuma aka ba Bawuro da Rabiu kashi 20% kowanne. Wannan shi ne lokacin da aka cire Jihar Kano gaba ɗaya daga cikin masu mallakar hannun jarin.

Kwangilar Biliyoyin Naira Da Kano Ta Biya Duk Da Ba Za Ta Amfana Ba

Bayan hannun jarin ya koma na ƴaƴansa, Ganduje, a matsayinsa na Gwamnan jihar, shi ya zartar da ƙwangilar gina wannan ababen more rayuwa da jihar Kano ya kamata ta gina tun 2006 a matsayin biyan hannun jarinta. A ranar 7 ga Yuli, 2020, an ba da kwangilar aikin gina waɗannan kayayyakin ga kamfanin FRI Construction Company Limited akan kuɗi kimanin Naira biliyan 2.3, wanda daga baya aka ƙara zuwa fiye da Naira biliyan 4.

Ma’ana, Ganduje ya ba da ƙwangilar aikin da jihar Kano ya kamata ta yi domin biyan hannun jarinta, amma a lokacin da aka ba da kwangilar, jihar ba ta da ko kashi 1% a cikin kamfanin, yayin da ƴaƴansa suka riƙe da kashi 60% tare da abokinsa Bawuro.

Yadda Aka Musanya Hannun Jarin Daga Ƴaƴansa Zuwa Abokinsa

Bayan shekaru biyu, a 2022, bayanan kamfanin a CAC sun nuna cewa an cire ƴaƴan Ganduje daga jerin masu hannun jari, an kuma miƙa hannun jarinsu ga Abubakar Bawuro. Wannan ya sa Bawuro ya zama mai kashi 80% na dukkan hannun jarin kamfanin, yayin da Ahmad Rabiu ya ke riƙe kashi 20%.

Jihar Kano Ta Nuna Rashin Jin Daɗi

Gwamnatin Jihar Kano ta yanzu, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta ƙi amincewa da wannan canjin mallakar. Wani jami’i a ma’aikatar kasuwanci ta jihar, Bashir Uba, ya tabbatar da cewa a bayanansa, jihar har yanzu tana da hannun jarinta na kashi 20%. Ya bayyana cewa ba a taba fitar da tallace-tallace ko nuna aniyar sayar da hannun jarin ba, sannan cewa haƙiƙa jihar na neman ƙara hannun jarinta a kamfanin, ba ragewa ba.

Ya kuma ce ma’aikatun jihar na gudanar da bincike kan yadda Bawuro ya sami ikon mallakar kashi 80% na kamfanin.

Keta Dokoki

Masana a fannin shari’a sun bayyana cewa, duk wani yunƙuri na sayar da hannun jarin jihar dole ne ya bi tsarin doka wanda ya haɗa da amincewa da izinin majalisar jihar, da kuma fitar da tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai na ƙasa domin neman masu saye. Binciken ya nuna cewa ba a bi wannan tsari ba, wanda ke nuna cewa an yi wannan musayar mallaka ne a asirce kuma ba bisa ƙa’ida ba.

Ganduje
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.