ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
Ganduje

Wani binciken jaridar Premium Times na musamman ya tona asirin irin yadda tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya janye hannun jihar daga kamfanin Dala Inland Dry Port Limited, inda ya mayar da hannun jarin jihar ga ƴaƴansa, kafin ya ba da kwangilar aikin gina kayayyakin more rayuwa a tashar akan biliyoyin Naira.

Binciken da aka yi ya nuna cewa, a shekarar 2020, Gwamna Ganduje ya yi wata yarjejeniya a asirce wadda ya musanya hannun jarin Kano na kashi 20 cikin 100 a kamfanin Dala Inland Dry Port, ya kuma sanya ƴaƴansa uku – Abdulaziz, Umar, da Muhammad Abdullahi Umar – a matsayin masu hannun jari kuma daraktocin kamfanin.

  • Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 
  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Yadda Aka Fara Maganar Hannun Jarin

ADVERTISEMENT

A shekarar 2006, lokacin mulkin Gwamna Ibrahim Shekarau, Jihar Kano ta sayi hannun jari na kashi 20% a kamfanin Dala Inland Dry Port. Yarjejeniyar ta tanadi cewa jihar za ta biya kuɗin hannun jarin ta ne ta hanyar gina ababen more rayuwa kamar hanyoyi, wutar lantarki, da samar da ruwa a wurin da ake ginawa a Zawachiki, Kano.

Sai dai, gwamnonin da suka gabace shi, Shekarau da Rabiu Kwankwaso, ba su yi wani aikin da yarjejeniyar ta tanada ba  na gina waɗannan kayayyakin ba. Wannan rashin aiki ya kai ga cewa Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Nijeriya (Nigerian Shippers’ Council) ta yi barazanar soke yarjejeniyar da kamfanin a shekarar 2019 saboda rashin cimma yarjejeniyar mallakar.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Shigowar Ganduje Da Sauya Mallaka A Asirce

Sakamakon barazanar soke yarjejeniyar ya sa dole wanda ya kafa kamfanin, Ahmad Rabiu, ya nemi sabon abokin tarayya. A cikin wannan lokacin ne, a ranar 5 ga Maris, 2020, aka gudanar da wani taro na musamman na kamfanin Dala Inland Dry Port.

A cikin wannan taron, an cire duk tsoffin daraktocin kamfanin, an kuma naɗa ƴaƴan Ganduje uku da wani ɗan nasa na kut da kut mai suna Abubakar Bawuro, a matsayin sabbin daraktoci. An ba kowane ɗaya daga cikin ƴaƴan Ganduje hannun jari na kashi 20% kowanne, haka kuma aka ba Bawuro da Rabiu kashi 20% kowanne. Wannan shi ne lokacin da aka cire Jihar Kano gaba ɗaya daga cikin masu mallakar hannun jarin.

Kwangilar Biliyoyin Naira Da Kano Ta Biya Duk Da Ba Za Ta Amfana Ba

Bayan hannun jarin ya koma na ƴaƴansa, Ganduje, a matsayinsa na Gwamnan jihar, shi ya zartar da ƙwangilar gina wannan ababen more rayuwa da jihar Kano ya kamata ta gina tun 2006 a matsayin biyan hannun jarinta. A ranar 7 ga Yuli, 2020, an ba da kwangilar aikin gina waɗannan kayayyakin ga kamfanin FRI Construction Company Limited akan kuɗi kimanin Naira biliyan 2.3, wanda daga baya aka ƙara zuwa fiye da Naira biliyan 4.

Ma’ana, Ganduje ya ba da ƙwangilar aikin da jihar Kano ya kamata ta yi domin biyan hannun jarinta, amma a lokacin da aka ba da kwangilar, jihar ba ta da ko kashi 1% a cikin kamfanin, yayin da ƴaƴansa suka riƙe da kashi 60% tare da abokinsa Bawuro.

Yadda Aka Musanya Hannun Jarin Daga Ƴaƴansa Zuwa Abokinsa

Bayan shekaru biyu, a 2022, bayanan kamfanin a CAC sun nuna cewa an cire ƴaƴan Ganduje daga jerin masu hannun jari, an kuma miƙa hannun jarinsu ga Abubakar Bawuro. Wannan ya sa Bawuro ya zama mai kashi 80% na dukkan hannun jarin kamfanin, yayin da Ahmad Rabiu ya ke riƙe kashi 20%.

Jihar Kano Ta Nuna Rashin Jin Daɗi

Gwamnatin Jihar Kano ta yanzu, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta ƙi amincewa da wannan canjin mallakar. Wani jami’i a ma’aikatar kasuwanci ta jihar, Bashir Uba, ya tabbatar da cewa a bayanansa, jihar har yanzu tana da hannun jarinta na kashi 20%. Ya bayyana cewa ba a taba fitar da tallace-tallace ko nuna aniyar sayar da hannun jarin ba, sannan cewa haƙiƙa jihar na neman ƙara hannun jarinta a kamfanin, ba ragewa ba.

Ya kuma ce ma’aikatun jihar na gudanar da bincike kan yadda Bawuro ya sami ikon mallakar kashi 80% na kamfanin.

Keta Dokoki

Masana a fannin shari’a sun bayyana cewa, duk wani yunƙuri na sayar da hannun jarin jihar dole ne ya bi tsarin doka wanda ya haɗa da amincewa da izinin majalisar jihar, da kuma fitar da tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai na ƙasa domin neman masu saye. Binciken ya nuna cewa ba a bi wannan tsari ba, wanda ke nuna cewa an yi wannan musayar mallaka ne a asirce kuma ba bisa ƙa’ida ba.

Ganduje
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.