ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ganduje Ya Janye Hannun Jarin Jihar Kano, Ya Saka Ƴaƴansa 3 A Dala Inland Dry Port

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Ganduje

Wani binciken jaridar Premium Times na musamman ya tona asirin irin yadda tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya janye hannun jihar daga kamfanin Dala Inland Dry Port Limited, inda ya mayar da hannun jarin jihar ga ƴaƴansa, kafin ya ba da kwangilar aikin gina kayayyakin more rayuwa a tashar akan biliyoyin Naira.

Binciken da aka yi ya nuna cewa, a shekarar 2020, Gwamna Ganduje ya yi wata yarjejeniya a asirce wadda ya musanya hannun jarin Kano na kashi 20 cikin 100 a kamfanin Dala Inland Dry Port, ya kuma sanya ƴaƴansa uku – Abdulaziz, Umar, da Muhammad Abdullahi Umar – a matsayin masu hannun jari kuma daraktocin kamfanin.

  • Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 
  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Yadda Aka Fara Maganar Hannun Jarin

ADVERTISEMENT

A shekarar 2006, lokacin mulkin Gwamna Ibrahim Shekarau, Jihar Kano ta sayi hannun jari na kashi 20% a kamfanin Dala Inland Dry Port. Yarjejeniyar ta tanadi cewa jihar za ta biya kuɗin hannun jarin ta ne ta hanyar gina ababen more rayuwa kamar hanyoyi, wutar lantarki, da samar da ruwa a wurin da ake ginawa a Zawachiki, Kano.

Sai dai, gwamnonin da suka gabace shi, Shekarau da Rabiu Kwankwaso, ba su yi wani aikin da yarjejeniyar ta tanada ba  na gina waɗannan kayayyakin ba. Wannan rashin aiki ya kai ga cewa Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Nijeriya (Nigerian Shippers’ Council) ta yi barazanar soke yarjejeniyar da kamfanin a shekarar 2019 saboda rashin cimma yarjejeniyar mallakar.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Shigowar Ganduje Da Sauya Mallaka A Asirce

Sakamakon barazanar soke yarjejeniyar ya sa dole wanda ya kafa kamfanin, Ahmad Rabiu, ya nemi sabon abokin tarayya. A cikin wannan lokacin ne, a ranar 5 ga Maris, 2020, aka gudanar da wani taro na musamman na kamfanin Dala Inland Dry Port.

A cikin wannan taron, an cire duk tsoffin daraktocin kamfanin, an kuma naɗa ƴaƴan Ganduje uku da wani ɗan nasa na kut da kut mai suna Abubakar Bawuro, a matsayin sabbin daraktoci. An ba kowane ɗaya daga cikin ƴaƴan Ganduje hannun jari na kashi 20% kowanne, haka kuma aka ba Bawuro da Rabiu kashi 20% kowanne. Wannan shi ne lokacin da aka cire Jihar Kano gaba ɗaya daga cikin masu mallakar hannun jarin.

Kwangilar Biliyoyin Naira Da Kano Ta Biya Duk Da Ba Za Ta Amfana Ba

Bayan hannun jarin ya koma na ƴaƴansa, Ganduje, a matsayinsa na Gwamnan jihar, shi ya zartar da ƙwangilar gina wannan ababen more rayuwa da jihar Kano ya kamata ta gina tun 2006 a matsayin biyan hannun jarinta. A ranar 7 ga Yuli, 2020, an ba da kwangilar aikin gina waɗannan kayayyakin ga kamfanin FRI Construction Company Limited akan kuɗi kimanin Naira biliyan 2.3, wanda daga baya aka ƙara zuwa fiye da Naira biliyan 4.

Ma’ana, Ganduje ya ba da ƙwangilar aikin da jihar Kano ya kamata ta yi domin biyan hannun jarinta, amma a lokacin da aka ba da kwangilar, jihar ba ta da ko kashi 1% a cikin kamfanin, yayin da ƴaƴansa suka riƙe da kashi 60% tare da abokinsa Bawuro.

Yadda Aka Musanya Hannun Jarin Daga Ƴaƴansa Zuwa Abokinsa

Bayan shekaru biyu, a 2022, bayanan kamfanin a CAC sun nuna cewa an cire ƴaƴan Ganduje daga jerin masu hannun jari, an kuma miƙa hannun jarinsu ga Abubakar Bawuro. Wannan ya sa Bawuro ya zama mai kashi 80% na dukkan hannun jarin kamfanin, yayin da Ahmad Rabiu ya ke riƙe kashi 20%.

Jihar Kano Ta Nuna Rashin Jin Daɗi

Gwamnatin Jihar Kano ta yanzu, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta ƙi amincewa da wannan canjin mallakar. Wani jami’i a ma’aikatar kasuwanci ta jihar, Bashir Uba, ya tabbatar da cewa a bayanansa, jihar har yanzu tana da hannun jarinta na kashi 20%. Ya bayyana cewa ba a taba fitar da tallace-tallace ko nuna aniyar sayar da hannun jarin ba, sannan cewa haƙiƙa jihar na neman ƙara hannun jarinta a kamfanin, ba ragewa ba.

Ya kuma ce ma’aikatun jihar na gudanar da bincike kan yadda Bawuro ya sami ikon mallakar kashi 80% na kamfanin.

Keta Dokoki

Masana a fannin shari’a sun bayyana cewa, duk wani yunƙuri na sayar da hannun jarin jihar dole ne ya bi tsarin doka wanda ya haɗa da amincewa da izinin majalisar jihar, da kuma fitar da tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai na ƙasa domin neman masu saye. Binciken ya nuna cewa ba a bi wannan tsari ba, wanda ke nuna cewa an yi wannan musayar mallaka ne a asirce kuma ba bisa ƙa’ida ba.

Ganduje
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Ƙungiyar PENGASSAN Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.