Shugaban ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya kuma gwamnan Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin mafi karancin albashi zuwa ₦100,000, yana mai cewa sauye-sauyen tattalin arziƙin gwamnati sun ƙara ƙarfin kuɗaɗen shiga na jihohi.
Gwamna AbdulRazaq ya bayyana hakan yayin taron gwamnoni da shugaba Tinubu, inda ya ce jihohi da dama da a baya ke dogaro da rance da fitar da takardun bashi domin gudanar da ayyuka yanzu sun fara rage basussukansu sakamakon ƙarin kuɗaɗen shiga bayan cire tallafin man fetur.
A cewarsa, ƙarin albashin zai dace da halin matsin rayuwa da ma’aikata ke fuskanta, yayin da gwamnoni ke ci gaba da tattaunawa da gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya mai dorewa.
A halin yanzu, mafi ƙarancin albashi na kasa a Nijeriya shi ne ₦70,000, wanda aka amince da shi tun shekarar 2024. Sai dai wasu jihohi sun riga sun fara biyan fiye da wannan adadi, yayin da ake ci gaba da kiraye-kirayen sake duba albashin saboda tsadar rayuwa da hauhawar farashi.















Discussion about this post