ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sha Gwagwarmaya A Matsayin Direban Taksi – Tinubu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bada labarin yadda wani Sojan ruwa ya sharara masa mari bisa tsula masa kudin fasinja fiye da yadda ake amsa ba da gangan ba a lokacin da yake direban Tasi a kasar Amurka. 

 

Wannan na kunshe ne cikin labarin yadda ya taso da rayuwarsa da aka wallafa a bayan manyan jaridun Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Tarihin rayuwar da aka masa take da ‘Tinubu: rayuwata a matsayin direban Taksi a Amurka’, da fitaccen dan jarida, Mike Awoyinfa, ya wallafa.

 

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

A cikin tarihin rayuwar Tinubun, ya ce, ya yi aiki a matsayin direban Taksin da baida lasisi a garin Chicago da ke Amurka inda ke aikin jigilar kwaso fasinjoji daga filin jirgin sama zuwa inda za su sauka.

 

Shugaban kasan ya ce ya kama sana’ar tuki ne da nufin samun kudin da zai rayu kafin ya tafi makaranta.

 

Ya nakalto, “Mun samu mota (da aka taba amfani da ita) da ba ta da rijista da ake kira Gypsy, wacce muke shiga da sunan kabu-kabu ‘taksi’. Muna kwasan fasinjoji daga filin jirgi mu kai su wurare amma ba ko’ina ba, kamar otel-otel saboda ba ko’ina ne motar da ba ta da lasisi ba za ta shiga.

 

“Muna yin hakan ne na ‘yan lokuta domin mu samu wasu ‘yan kudade. Bolaji ya tafi zuwa Tennessee, ni kuma na zarce zuwa Chicago.

 

“Ya kamata na fara zuwa makaranta a watan Afrilu. Amma na jingine har zuwa watan Satumba saboda na tara kudi. Zuwata Chicago ke da wuya, kai tsaye na wuce zuwa Kwalejin Richard Daley. Gwanin ban sha’awa.

 

“Na samu zarafin biyan kudin dakina da na kudin makaranta a jami’ar Chicago.”

 

Ya cigaba da bayanin yadda ta kaya da yadda wani Sojan ruwa ya taba marinsa a fuska saboda ya cajeshi kudin taksi da ya wuce inda ake amsa bisa kaisa wani wuri da ke kusa-kusa.

 

“A matsayina na direba, akwai wani abun da ba zan taba mancewa da shi ba, wani lokaci na fadi kudin Taksi ga wani Sojan ruwa da ya dawo cikin kasar fiye da adadin da ake karba na masa ‘tsada kenan’. Kuma ba da gangan na masa ba,” Tinubu ya bayyana.

 

“A zahirin gaskiya ni ban san wajen ba. Kuma babu wani dan GPRS a wadannan kwanakin balle wani ya kwatanta min wajen. Don haka, shi sojan shi ne ya kwatanta inda gidan nasa yake a wani unguwa a Virginia.

 

“Da na fada masa farashin kudin da zai biyani kwatsam amsar da zai ba ni shi ne sharara min mari a fuskata. Ya ce ya kamata na san hakikanin farashin zuwa wurin da ya fada min. Ya mareni ya ba ni kudin kuma.”

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Yadda Ake Sana’ar Canji

Yadda Ake Sana'ar Canji

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.