ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Sha Gwagwarmaya A Matsayin Direban Taksi – Tinubu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bada labarin yadda wani Sojan ruwa ya sharara masa mari bisa tsula masa kudin fasinja fiye da yadda ake amsa ba da gangan ba a lokacin da yake direban Tasi a kasar Amurka. 

 

Wannan na kunshe ne cikin labarin yadda ya taso da rayuwarsa da aka wallafa a bayan manyan jaridun Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Tarihin rayuwar da aka masa take da ‘Tinubu: rayuwata a matsayin direban Taksi a Amurka’, da fitaccen dan jarida, Mike Awoyinfa, ya wallafa.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

A cikin tarihin rayuwar Tinubun, ya ce, ya yi aiki a matsayin direban Taksin da baida lasisi a garin Chicago da ke Amurka inda ke aikin jigilar kwaso fasinjoji daga filin jirgin sama zuwa inda za su sauka.

 

Shugaban kasan ya ce ya kama sana’ar tuki ne da nufin samun kudin da zai rayu kafin ya tafi makaranta.

 

Ya nakalto, “Mun samu mota (da aka taba amfani da ita) da ba ta da rijista da ake kira Gypsy, wacce muke shiga da sunan kabu-kabu ‘taksi’. Muna kwasan fasinjoji daga filin jirgi mu kai su wurare amma ba ko’ina ba, kamar otel-otel saboda ba ko’ina ne motar da ba ta da lasisi ba za ta shiga.

 

“Muna yin hakan ne na ‘yan lokuta domin mu samu wasu ‘yan kudade. Bolaji ya tafi zuwa Tennessee, ni kuma na zarce zuwa Chicago.

 

“Ya kamata na fara zuwa makaranta a watan Afrilu. Amma na jingine har zuwa watan Satumba saboda na tara kudi. Zuwata Chicago ke da wuya, kai tsaye na wuce zuwa Kwalejin Richard Daley. Gwanin ban sha’awa.

 

“Na samu zarafin biyan kudin dakina da na kudin makaranta a jami’ar Chicago.”

 

Ya cigaba da bayanin yadda ta kaya da yadda wani Sojan ruwa ya taba marinsa a fuska saboda ya cajeshi kudin taksi da ya wuce inda ake amsa bisa kaisa wani wuri da ke kusa-kusa.

 

“A matsayina na direba, akwai wani abun da ba zan taba mancewa da shi ba, wani lokaci na fadi kudin Taksi ga wani Sojan ruwa da ya dawo cikin kasar fiye da adadin da ake karba na masa ‘tsada kenan’. Kuma ba da gangan na masa ba,” Tinubu ya bayyana.

 

“A zahirin gaskiya ni ban san wajen ba. Kuma babu wani dan GPRS a wadannan kwanakin balle wani ya kwatanta min wajen. Don haka, shi sojan shi ne ya kwatanta inda gidan nasa yake a wani unguwa a Virginia.

 

“Da na fada masa farashin kudin da zai biyani kwatsam amsar da zai ba ni shi ne sharara min mari a fuskata. Ya ce ya kamata na san hakikanin farashin zuwa wurin da ya fada min. Ya mareni ya ba ni kudin kuma.”

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Next Post
Yadda Ake Sana’ar Canji

Yadda Ake Sana'ar Canji

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.