ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za Ki Samu Karin Ni’ima Cikin Sauki

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
2 years ago
Karin Ni'ima

Assalamu alaikum masu karatu, barkan mu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Ado Da Kwalliya. A yau shafin namu zai muku bayani akan yadda za ki samu karin ni’ima.

Idan kina neman maganin karin ni’ima da ruwa to kin zo inda za ki samu.

Idan har kina so ruwan dadi da ni’ima su karu a jikin ki yadda za ki birge mijin lokacin saduwa.

ADVERTISEMENT

 

Zaki iya zabar hadi daya ki dinga yi kina sha:

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

Ga kadan daga cikin yadda a ke sarrafa wasu ruwan daga ciki:

Ruwan kankana, Ayaba Manya uku, kankana Kwata da Tuffa: Ki hada ki markada ki zuba madarar ruwa gwangwani daya, zuma yadda ki ke so, ki sa kankara ya yi sanyi, ki sha kamar lemo ke da maigida, yanada kyau sosai.

2- Ruwan tumatir: Ki markada tumatir biyu, ki zuba ruwan a cikin kwai uku, ki sa magi da albasa ki soya ya yi ruwa-ruwa ki ci, shi ma ya na saukar da ni’ima sosai da saka jin dadin auratayya, sannan hakan yana saka gogewar fata.

3- Ruwan Kwakwa: Ki fasa kwakwarki ki tsiyaye ruwan cikin kwakwar, sannan ki bare bakin bayan kwakwar ki goga kwakwar da magoki, sannan ki markada a ‘blander’, sai ki zuba ruwa a kan markadaddiyar kwakwar ki tace ruwan ki fid da dusar.

Da ma kin bare dabinonki cikin gwangwanin madarar ruwa daya, ki jika dabinon ya yi laushi sai ki markada ya yi laushi sosai, sai ki zuba a kan ruwan kwakwar, sannan ki zuba ruwan da ki ka fasa kwakwar ya zubo a ciki, ki zuba zuma da garin madara cokali uku a ciki, ki juya sosai. Ki sa a firij ya yi sanyi ko ki saka kankara. Idan ba ki son sanyi sai ki sha a haka. Ki yini ki na sha; kar ki barshi ya kwana. Ba zan ce komai ba, sai kin gwada kawai, uwargida za ki bada labari.

4- Ruwan Zogale: Amfanin ruwan Zogale ba zai lissafu ba a maganin cututtukan da ya ke yi a jikinmu. Amma zan yi bayanin amfaninsa a bangaren karin ni’ima a jikinmu ne kawai.

Ki tsinke zogale ki wanke ki tafasa sosai ki tace ruwan zogalen ki zuba kanumfari da Citta ki tafasa. Sai ki sauke ki dinga kurba da zafinsa kamar shayi. Ya na gyara jiki ya saukar da ni’ima sosai. Ya na kara wa mace kuzari a jikinta sosai, sannan ya na kara wa mace juriya wajen saduwa.

Ki tsinke zogale ki wanke ki markada ganyen a blander ko ki mutsuttsuka da hannunki ki kara ruwa a kai ki tace ki matse dusar ki zuba madarar ruwa gwangwani daya a cikin ruwan zogale ki sa a cikin Jug daya, ki sa zuma ta ji sosai, ki juya ya hadu ki dinga sha. Gaskiya ba shi da dadin sha, sai dai akwai shi da aiki; ni’ima lutsutsu! Domin duk bushewar gabanki da rashin ni’imarki sai ni’ima ta zo, kuma ya na sa jin dadi sosai.

7. Ruwan Dabino: Ki bare dabinonki rabin kwano, ki jika da ruwa, idan ya yi luguf sai ki markada a blander za ki gan shi da kauri kirtif, sai ki ajiye a firinji; duk sanda za ki sha sai ki debi cokali biyu ki zuba a kofi, ki juye madarar ruwa gwangwani daya, ki sa garin minannas karamin cokali ki juya sosai, idan ya yi kauri da yawa ki kara ruwa kadan ki kuma juyawa, ki shanye duka.

Bayan awa uku da shan ki za ki tsinci kanki cikin wani yanayi na lutsutsu da son kasancewa da maigidanki. Za ki ji dadin da ki ka dade ba ki ji ba, maigida kuwa zai gamsu da ke sosai.

6.Ruwan Rake: Ki bare rake ki yanka gutsi-gutsi ki daka a turmi ko ki markada a blander kina yi ki na kara ruwa a dusar raken kina matsewa. Idan kin sami ruwan rake kamar cikin jog daya. Sai ki sami ruwan tafasasshen baure jog daya sai ruwan jangari da jangagai da alewar mata da a ka tafasa su guri guda a ka tace su ma jog daya.

Sai ki zuba wannan ruwayen naki a wuta ki zuba zuma kofi daya ki yi ta dafawa har sai ruwan ya kone ya zama kamar cikin jug daya sai ki sauke amma za ki sa kanumfari da kayan kamshi a dahuwar idan ya huce sai ki juye a abu mai kyau ba zai lalalce ba. Kullum ki sha ludayi daya zai ratsa jikinki ki sami dauwamammiyar ni’ima maigida zai dinga jin gamsuwa da ke sosai. Tsimin rake kenan.

Karin Ni'ima
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
Karin Ni'ima
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

MASU ALAKA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Ado Da Kwalliya

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Ado Da Kwalliya

Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

May 17, 2026
Next Post
Eric Ten Hag: Ga Dara Ga Dare Ya Yi A Manchester United 

Eric Ten Hag: Ga Dara Ga Dare Ya Yi A Manchester United 

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.