ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: MDD Ta Yi Gargadin Mutum Miliyan 45 Za Su Fuskanci Karanci Abinci

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
MDD

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, ko shakka babu, miliyoyin mutane za su fuskanci matsananciyar yunwa, idan har yakin Amurka da Isra’ila a kan Iran ya ci gaba da kuma yadda Iran ta ke mayar da martani.

“Idan rikicin Gabas ta Tsakiya ya ci gaba har zuwa watan Yuni, za a iya tura karin mutane miliyan 45 cikin matsananciyar yunwa ta hanyar hauhawar farashin kayayyaki,” in ji Carl Skau, Mataimakin Babban Daraktan Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), wanda ya bayyana hakan a ranar Talatar da ta gabata.

  • Jajircewar Cardoso Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

“Wannan zai haifar  da wani mataki na karuwar yunwa a duniya fiye da kowane irin lokaci tarihi,” in ji Skau.

Hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, wanda ya fara a ranar 28 ga watan Fabrairu, ya danne muhimman hanyoyin bayar da agajin jin kai tare da jinkirta jigilar kayayyaki na ceton rai zuwa wasu munanan rikice-rikice a duniya.

Skau ya ce, farashin jigilar kayayyaki ya karu da kashi 18 cikin dari tun bayan da aka fara yakin, sannan kuma dole ne a samar da wasu hanyoyin.

Ya kara da cewa, karin kudin na zuwa ne sama da raguwar kashe kudade da WFP ke yi, yayin da masu bayar da taimako suka fi maida hankali a kan tsaro.

A Gaza, mazauna yankin na gaggawar tara kayayyaki a yayin da ake rufe kan iyaka da kuma yakin Iran da ke kara samar da karancin kayan masarufi, yayin da karancin kayayyaki ke kara ta’azzara a yankin da aka yi wa kawanya, yayin da Isra’ila ke ci gaba da yakin kisan kare dangi a can.

Isra’ila za ta sake bude wani bangare na mashigar Rafah ta Gaza da Masar a ranar Laraba, wanda ya kawo karshen rufewar makwanni biyu da ta yi, wanda ya dada zurfafa rikicin jin kai a yankin da ya lalace.

Isra’ila ta rufe mashigar a wannan rana, sannan kuma Amurka ta kai hare-hare kan Iran, saboda dalilai na tsaro.

Daraktan yanki na Hukumar Lafiya ta Duniya na Gabashin Bahar Rum, ya yi gargadin a makon da ya gabata cewa, kusan manyan motoci 200 ne ke shiga Gaza a kowace rana, wanda ya yi kasa da kiyasin da ake bukata na yau da kullum na 600.

A halin da ake ciki, sama da mutane miliyan 21 a Sudan, kusan rabin al’ummar kasar na fuskantar matsananciyar yunwa. An tabbatar da cewa, ana fama da yunwa a yankunan da aka kwashe watanni ana gwabzawa, ya sanya ba za a iya kai wa ga ma’aikatan agaji ba.

A watan Janairu, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, agajin da ake bai wa Sudan zai iya karewa cikin ‘yan watanni, matukar ba a yi alkawarin karin daruruwan miliyoyin daloli ba.

Tsawon shekara uku da aka kwashe ana gwabza kazamin yaki tsakanin gwamnatin mulkin soja da dakarun sa kai na gaggawa, ya yi sanadiyyar kisan dubunnan mutane tare da raba kimanin mutum miliyan 14 da muhallansu.

MDD
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.