ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: MDD Ta Yi Gargadin Mutum Miliyan 45 Za Su Fuskanci Karanci Abinci

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
MDD

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, ko shakka babu, miliyoyin mutane za su fuskanci matsananciyar yunwa, idan har yakin Amurka da Isra’ila a kan Iran ya ci gaba da kuma yadda Iran ta ke mayar da martani.

“Idan rikicin Gabas ta Tsakiya ya ci gaba har zuwa watan Yuni, za a iya tura karin mutane miliyan 45 cikin matsananciyar yunwa ta hanyar hauhawar farashin kayayyaki,” in ji Carl Skau, Mataimakin Babban Daraktan Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), wanda ya bayyana hakan a ranar Talatar da ta gabata.

  • Jajircewar Cardoso Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

“Wannan zai haifar  da wani mataki na karuwar yunwa a duniya fiye da kowane irin lokaci tarihi,” in ji Skau.

Hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, wanda ya fara a ranar 28 ga watan Fabrairu, ya danne muhimman hanyoyin bayar da agajin jin kai tare da jinkirta jigilar kayayyaki na ceton rai zuwa wasu munanan rikice-rikice a duniya.

Skau ya ce, farashin jigilar kayayyaki ya karu da kashi 18 cikin dari tun bayan da aka fara yakin, sannan kuma dole ne a samar da wasu hanyoyin.

Ya kara da cewa, karin kudin na zuwa ne sama da raguwar kashe kudade da WFP ke yi, yayin da masu bayar da taimako suka fi maida hankali a kan tsaro.

A Gaza, mazauna yankin na gaggawar tara kayayyaki a yayin da ake rufe kan iyaka da kuma yakin Iran da ke kara samar da karancin kayan masarufi, yayin da karancin kayayyaki ke kara ta’azzara a yankin da aka yi wa kawanya, yayin da Isra’ila ke ci gaba da yakin kisan kare dangi a can.

Isra’ila za ta sake bude wani bangare na mashigar Rafah ta Gaza da Masar a ranar Laraba, wanda ya kawo karshen rufewar makwanni biyu da ta yi, wanda ya dada zurfafa rikicin jin kai a yankin da ya lalace.

Isra’ila ta rufe mashigar a wannan rana, sannan kuma Amurka ta kai hare-hare kan Iran, saboda dalilai na tsaro.

Daraktan yanki na Hukumar Lafiya ta Duniya na Gabashin Bahar Rum, ya yi gargadin a makon da ya gabata cewa, kusan manyan motoci 200 ne ke shiga Gaza a kowace rana, wanda ya yi kasa da kiyasin da ake bukata na yau da kullum na 600.

A halin da ake ciki, sama da mutane miliyan 21 a Sudan, kusan rabin al’ummar kasar na fuskantar matsananciyar yunwa. An tabbatar da cewa, ana fama da yunwa a yankunan da aka kwashe watanni ana gwabzawa, ya sanya ba za a iya kai wa ga ma’aikatan agaji ba.

A watan Janairu, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, agajin da ake bai wa Sudan zai iya karewa cikin ‘yan watanni, matukar ba a yi alkawarin karin daruruwan miliyoyin daloli ba.

Tsawon shekara uku da aka kwashe ana gwabza kazamin yaki tsakanin gwamnatin mulkin soja da dakarun sa kai na gaggawa, ya yi sanadiyyar kisan dubunnan mutane tare da raba kimanin mutum miliyan 14 da muhallansu.

MDD
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

MDD
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
MDD
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
MDD
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.