ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: MDD Ta Yi Gargadin Mutum Miliyan 45 Za Su Fuskanci Karanci Abinci

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
MDD

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, ko shakka babu, miliyoyin mutane za su fuskanci matsananciyar yunwa, idan har yakin Amurka da Isra’ila a kan Iran ya ci gaba da kuma yadda Iran ta ke mayar da martani.

“Idan rikicin Gabas ta Tsakiya ya ci gaba har zuwa watan Yuni, za a iya tura karin mutane miliyan 45 cikin matsananciyar yunwa ta hanyar hauhawar farashin kayayyaki,” in ji Carl Skau, Mataimakin Babban Daraktan Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), wanda ya bayyana hakan a ranar Talatar da ta gabata.

  • Jajircewar Cardoso Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

“Wannan zai haifar  da wani mataki na karuwar yunwa a duniya fiye da kowane irin lokaci tarihi,” in ji Skau.

Hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, wanda ya fara a ranar 28 ga watan Fabrairu, ya danne muhimman hanyoyin bayar da agajin jin kai tare da jinkirta jigilar kayayyaki na ceton rai zuwa wasu munanan rikice-rikice a duniya.

Skau ya ce, farashin jigilar kayayyaki ya karu da kashi 18 cikin dari tun bayan da aka fara yakin, sannan kuma dole ne a samar da wasu hanyoyin.

Ya kara da cewa, karin kudin na zuwa ne sama da raguwar kashe kudade da WFP ke yi, yayin da masu bayar da taimako suka fi maida hankali a kan tsaro.

A Gaza, mazauna yankin na gaggawar tara kayayyaki a yayin da ake rufe kan iyaka da kuma yakin Iran da ke kara samar da karancin kayan masarufi, yayin da karancin kayayyaki ke kara ta’azzara a yankin da aka yi wa kawanya, yayin da Isra’ila ke ci gaba da yakin kisan kare dangi a can.

Isra’ila za ta sake bude wani bangare na mashigar Rafah ta Gaza da Masar a ranar Laraba, wanda ya kawo karshen rufewar makwanni biyu da ta yi, wanda ya dada zurfafa rikicin jin kai a yankin da ya lalace.

Isra’ila ta rufe mashigar a wannan rana, sannan kuma Amurka ta kai hare-hare kan Iran, saboda dalilai na tsaro.

Daraktan yanki na Hukumar Lafiya ta Duniya na Gabashin Bahar Rum, ya yi gargadin a makon da ya gabata cewa, kusan manyan motoci 200 ne ke shiga Gaza a kowace rana, wanda ya yi kasa da kiyasin da ake bukata na yau da kullum na 600.

A halin da ake ciki, sama da mutane miliyan 21 a Sudan, kusan rabin al’ummar kasar na fuskantar matsananciyar yunwa. An tabbatar da cewa, ana fama da yunwa a yankunan da aka kwashe watanni ana gwabzawa, ya sanya ba za a iya kai wa ga ma’aikatan agaji ba.

A watan Janairu, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, agajin da ake bai wa Sudan zai iya karewa cikin ‘yan watanni, matukar ba a yi alkawarin karin daruruwan miliyoyin daloli ba.

Tsawon shekara uku da aka kwashe ana gwabza kazamin yaki tsakanin gwamnatin mulkin soja da dakarun sa kai na gaggawa, ya yi sanadiyyar kisan dubunnan mutane tare da raba kimanin mutum miliyan 14 da muhallansu.

MDD
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.