Majalisar Ƙoli ta Shari’a ta yi watsi da zargin da ke cikin ƙudirin dokar Majalisar Dokokin Amurka cewa ana kashe Kiristoci a Nijeriya, tana mai cewa zargin ba gaskiya ba ne kuma yana da hatsari.
Wasu ‘yan majalisar Amurka sun gabatar da ƙudirinnl ƙaƙaba takunkumi, ciki har da hana biza da ƙwace kadarori, ga mutanen da ake zargi da taimaka wa ta’addanci.
- Hedikwatar Tsaro Ta Tabbatar Da Isowar Sojojin Amurka A Jihar Bauchi
- Ramadan: Shehu Ismaila Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Kaduna
Cikin waɗanda aka ambata akwai Rabiu Musa Kwankwaso da kuma Miyetti Allah.
A sanarwar da Sakataren Janar na majalisar, Nafiu Baba Ahmad ya sanya wa hannu, majalisar ta ce Nijeriya na fuskantar matsalolin tsaro kamar ta’addanci da fashi, amma babu wata manufa da ta shafi kai wa Kiristoci hari.
Sanarwar ta kuma yi watsi da zargin da Amurka ta yi wa tsohon gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso na hannu a gallaza wa Kiristoci.
Ta kuma yi gargaɗin cewa kiran matsalar da “kisan kare dangi” zai iya ƙara tayar da hankali, tare da kira ga a yanke hukunci bisa sahihan bayanai da haɗin gwiwa da hukumomin Nijeriya.
Ta ƙara da cewa Musulmi da Kiristoci duka suna sha wahala sakamakon tashin hankali.















Discussion about this post