ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
9 months ago
Wasan Afirka

Tuni aka fara kakar wasa ta shekara ta 2025 zuwa 2026 ta gasar Premier League ta Ingila inda aka ci gaba a ranar Juma’a 14 ga watan Agustan wannan shekarar kuma mai kare kambu, kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ce ta fara wasa a gida a wasan da ta doke kungiyar kwallon kafa ta Bournemouth da ci 3-2 a filin was ana Anfield dake birnin Liberpool.

 

Tauraron danwasan kasar Masar Mohamed Salah, shi ne gwarzon danwasan gasar kuma zai yi yunkurin lashe takalmin zinare na biyar yayin da zai fara buga wasa da sababbin ‘yanwasan da kungiyar ta saya da suka hada da Hugo Ekitike da Florian Wirtz da Jeremi Frimpong da Leon da Milos Kerkez.

ADVERTISEMENT
  • Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?
  • Xi: Har Kullum Sin Za Ta Kasance Amintacciyar Abokiyar Huldar MDD

Wasu ‘yanwasan Afirka da dama sun samu komawa manyan kungiyoyi, akwai kuma wasu sababbi a gasar daga kasashen Kongo, da Morocco, da Mozambikue, da Senegal. A gefe guda kuma, ‘yanwasan nahiyar kusan 50 ne za su bar wasannin gasar zuwa gida domin karawa a gasar Kofin kasashen Afirka ta 2025 (Afcon 2025) da za a yi daga 21 ga watan Disamba zuwa 18 ga Janairu.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Ko Mbeumo zai dawo wa United da karsashinta?

Dan wasan dan kasar Kamaru Bryna Mbeumo ya zama abin tattaunawa kuma mafi tsada a ‘yanwasan Afirka lokacin da ya koma Manchester United kan fani miliyan 65 daga kungiyar kwallon kafa ta Brentford. Dan kwallon mai shekara 25 ya ci kwallo 20 a gasar da aka kammala da kuma bayarwa a ci bakwai. Manchester United na tsaka da sake gina kungiyar karkashin mai horarwa Ruben Amorim bayan gama gasar a mataki na 15, wanda shi ne mafi muni a tarihin kungiyar na Premier League.

Mbeumo zai fuskanci matsi nan take domin ya nuna kwarewarsa tare da Matheus Cunha da Benjamin Sesko wadanda duka kungiyar ta sayo a wannan kakar domin kara karfin ‘yanwasan gabanra da kuma kokarin ci gaba da zura kwallaye a raga duk da cewa bayan buga wasanni biyu a gasar firimiya har yanzu babu daya daga cikinsu da ya zura kwallo a raga.

Wani babban cinikin da aka yi shi ne wanda dan wasa Mohammed Kudus ya kawo karshen zaman shekara biyu da ya yi a kungiyar West Ham kuma ya koma Tottenham kan fan miliyan 55. Danwasan na Ghana ya taka rawa sosai a West Ham a kakar farko, amma bai yi kokari ba a kaka ta biyu saboda yadda ya yi fama da salon wasa na mai horarwa Graham Potter.

Irin kokarin da dan wasan mai shekara 24 din ya yi shi ne ya sa kungiyoyi da dama suka dinga nemansa, kuma yanzu Tottenham za ta so ya nemo wannan bajintar tasa domin taimaka mata a sabuwar kaka. Saboda samun damar buga gasar zakarun Turai ta Champions League na daya daga cikin dalilan da suka sa ya koma kungiyar Tottenham ta birnin London.

Yayin da tauraron danwasa Son Heung-Min ya bar kungiyar, da kuma James Maddison da ya ji rauni, Kudus zai iya zama mai muhimmancin gaske tun daga farkon kaka.

 

Ko Ait-Nouri zai taimaki Man City dawo da martabarta?

Bayan komawa mataki na uku da kuma kammala kakar 2024 zuwa 2025 ba tare da wani kofin kirki ba, Manchester City za ta danno da karfinta domin daukar kofi. Kungiyar ta shiga kasuwa da wurwuri domin daukar danwasan baya daga bangaren hagu Rayan Ait-Nouri, kuma danwasan mai shekara 24 ya fara buga mata wasa a gasar Club World Cup da ba ta je ko’ina ba. Dab wasan dan kasar Aljeriya ya koma Manchester City ne daga Wolbes a kan kudi fam miliyan 31.

Ait-Nouri ya nuna barazanar kai hari sosai daga gefensa duk da yadda Wolbes ta sha fama a kakar bara, inda ya ci kwallo hudu da kuma bayar da bakwai a zira a raga. Bayan ya samu wuri a Manchester City, tabbas mai horarwa Pep Guardiola zai so sabon mutumin nasa ya kara wuta wajen jawo kwallo daga baya zuwa gaba, sai dai bai taimakawa kungiyar ba a wasan da suka yi Rashin nasara a hannun Tottenham a ranar Asabar.

Adingra a Sunderland. Kungiyar Sunderland ta dawo buga gasar Premier League a karon farko tun 2017, kuma tuni ta karade kasuwar sayen ‘yanwasa, har ma ta sayi 11.

Shida daga cikinsu ‘yan Afirka ne. Ta kashe kudi mafi yawa a tarihinta fan miliyan 30 kan dan kasar Senegal Habib Diarra, da daukar Arthur Masuaku da Noah Sadiki ‘yan kasar Kongo, da dan Mozambikue mai suna Reinildo, da Chemsdine Talbi na Morocco.

Simon Adingra da ya ci kofin Afcon 2023 da kasarsa Ibory Coast na cikin mutanen da ya sauya sheka daga kudu zuwa arewaci bayan fara wasa 12 kacal a kakar bara. Yayin da yake cikin ‘yanwsan da suka san Premier League, dan kwallon mai shekara 23 zai so ya taimaka wa Sunderland ci gaba da zama a gasar.

Har yanzu West Ham za ta ci gaba da aiki da dan Afirka bayan ta biya fan miliyan 19 wajen daukar El Hadji Malick Diouf daga Slabia Prague.

Kociyan kungiyar Graham Potter ya ce dan wasan Senegal din mai shekara 20 yana da yunwar buga wasa da kuma buri mai yawa saboda haka za su taimaka masa wajen cika burinsa kuma West Ham United ce kungiyar da zai samu wannan damar.

Shima danwasan Kongo Aedel Tuanzebe zai so ya sake guje wa barin gasar ta Premier a karo na biyu bayan ya koma Burnley daga Ipswich Town. Ganin cewa sai a ranar 1 ga watan Satumba za a rufe kasuwar saye da musayar ‘yan kwallon, akwai ‘yanwasan Afirka da za su motsa a bana zuwa Premier.

Dan wasan Senegal da Chelsea, Nicolas Jackson ya samu izinin barin Chelsea a kasuwar nan, yayin da shi ma na Kongo Yoane Wissa ke shirin barin Brentford zuwa Newcastle United.

Wasan Afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
Wasan Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.