• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasan Da Suka Fi Tsada A Duniya Yanzu

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
‘Yan Wasan Da Suka Fi Tsada A Duniya Yanzu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matasan ‘yan wasan da suka hada da Kylian Mbappe, Binicius Jr da kuma Erling Haaland su ne ‘yan wasan da suka fi tsada a duniya, a cewar wani bincike da Cibiyar Da Ke Nazari Kan Harkokin Kwallon Kafa, (CIES) Football Observatory ta gudanar.

Mbappe, mai shekara 23 a duniya, wanda ya ki amincewa ya komai Real Madrid ya gwammace ci gaba da zama a Paris St-German, shi ne kan gaba a cikin ‘yan wasa mafi tsada a duniya inda darajarsa ta kai yuro miliyan 205.6.

  • Dembele Ya Amince Da Komawa Chelsea Daga Barcelona

Dan wasan Real Madrid dan kasar Brazil Binicius Jr, wanda ya zura kwallon da ta ba su nasara a wasan karshe na gasar Zakarun Turai da suka fafata da Liverpool, shi ne na biyu mafi tsada wanda darajarsa ta kai Yuro miliyan 158.3, yayin da dan kasar Norway da ke buga wasa a Manchester City Haaland shi ne na uku inda ya kai Yuro miliyan 130.4.

Dan wasan tsakiya na Borussia Dortmund Jude Bellingham (£114.1m) shi ne dan kasar Ingila mafi tsada inda yake a matsayi na biyar a wannan jadawali, inda yake gaban takwaransa na Ingila kuma dan wasan Manchester City Phil Foden, wanda yake matsayi na shida Yuro miliyan miliyan 105.9.
Kungiyoyin da ke fafatawa a Gasar Firimiya su ne suka kankame jerin ‘yan wasan da suka fi tsada inda ‘yan wasa 41 suka fito a cikin ‘yan wasan 100 da suka fi daraja kamar yadda binciken ya tabbatar.
CIES ta yi amfani da wasu muhimman abubuwa, da suka hada da shekarun dan wasa, kwazonsa da tattalin arzikin kungiyarsa da kuma hauhuawar farashi wajen gudanar da wannan bincike da ake yi.
Dan wasan Faransa Mbappe ya sanya hannu kan kwantaragin shekaru uku a kungiyarsa ta PSG a watan jiya yayin da ya zabi ci gaba da zama a kungiyar ta Paris maimakon tafiya kungiyar Real Madrid.

‘Yan wasa 10 mafi tsada a duniya
Kylian Mbappe – Paris St-Germain – Yuro miliyan 175.7. Sai kuma Binicius Jr- Real Madrid – Yuro miliyan 158.3. Erling Haaland – Borussia Dortmund kuma Yuro miliyan 130.4. Sannan Pedri – Barcelona Yuro miliyan 115.4. Akwai Jude Bellingham na Borussia Dortmund – shi kuma Yuro miliyan 114.2. Phil Foden – Manchester City – Yuro miliyan 105.9. Frenkie de Jong – Yuro miliyan Barcelona- 96.1. Luis Diaz – Liverpool – Yuro miliyan 94.0. Ruben Diaz – Manchester City – Yuro miliyan 93.6. Ferran Torres – Barcelona – Yuro miliyan 93.5.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Ya Kamata Mane Ya Bar Liverpool?

Next Post

Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

2 hours ago
Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad
Wasanni

Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad

10 hours ago
Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final
Wasanni

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

14 hours ago
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund
Wasanni

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

15 hours ago
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford
Wasanni

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

17 hours ago
Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata
Wasanni

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

18 hours ago
Next Post
Arewa

Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.