Rahotanni daga shirin Sunday Politics na Channels Television sun tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta samu nasarar karbo dalibai 100 daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su a makarantar St. Mary’s Private Catholic School da ke Papiri, karamar hukumar Agwara a jihar Neja.
Duk da wannan ci gaba, ba a samu cikakkiyar sanarwa daga gwamnatin tarayya ko ta jihar ba a hukumance har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
An sace ɗaliban ne a safiyar ranar 21 ga Nuwamba, 2025, lokacin da ’yan bindiga suka kutsa makarantar da misalin ƙarfe 2 na dare, inda suka mamaye ɗakunan kwanan dalibai na tsawon kusan sa’o’i uku. Jimillar mutane 315 aka sace, ciki har da ɗalibai 303 da malamai 12, kafin jami’an tsaro da yan sa-kai su fara bin sawun masu garkuwa da su a dazuzzukan da ke makwabtaka.
- Makonni Biyu Bayan Sace Ɗaliban Makarantar Papiri A Neja, Har Yanzu Babu Tuntuɓa
- Dambarwar Amurka Da Sace ‘Yan Makarantar Kebbi Da Neja: Shugaba Tinubu Ya Yi Rawar Gani
Bayan awanni 24 da faruwar harin, ɗalibai 50 sun tsere daga hannun masu garkuwar kuma an mayar da su ga iyalansu. Gwamnatin Tarayya ta yi gaggawar saka dokar ta baci ta musamman a yankin tare da baza jiragen sintiri na sama da wasu sassan Neja, da Kwara da Kebbi. Haka kuma Shugaba Bola Tinubu ya soke wasu tafiye-tafiye na ƙasashen waje domin kula da matakan ceto daliban kai tsaye.
Daga bisani, hukumomi suka bada umarnin rufe dukkan makarantun jihar Neja da wasu manyan makarantun tarayya da ke cikin yankunan da ke fuskantar matsalar tsaro. Ana sa ran ƙarin bayani a hukumance nan ba da jimawa ba.














