ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
Majalisa

Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu na neman bashi daga ƙasashen waje da ya haura dala biliyan 21 domin aiwatar da kasafin kuɗin shekarar 2025 zuwa 2026.

Majalisar ta bayyana cewa za a yi amfani da bashin ne wajen aiwatar da muhimman ayyukan ci gaban ƙasa, musamman a fannonin ababen more rayuwa, da tsaro, da noma da kuma gina ɗan Adam.

  • Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro

Da yake gabatar da rahoton a zauren majalisa yau Talata, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan basussukan cikin gida da na waje, Sanata Aliyu Wamako, ya ce an jinkirta amincewar rahoton ne saboda hutu na majalisa da kuma jinkiri wajen samun takardun daga Ofishin Kula da Basussuka (DMO).

ADVERTISEMENT

Bashin da aka amince da su sun haɗa da:

Dala biliyan 21.19 na bashin kai tsaye daga ƙetare

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Yuro biliyan 4

Yen biliyan 15 (na Japan)

Tallafin dala miliyan 65

Kuma aron cikin gida ta hanyar sayar da hannun jarin gwamnati (bond) na kusan Naira biliyan 757.

Har ila yau, akwai shirin tara kuɗi har dala biliyan 2 ta hanyar takardun lamuni da za a fitar cikin ƙasa amma a kuɗin ƙetare.

Shugaban kwamitin kasafi, Sanata Olamilekan Solomon, ya ce wannan amincewa tsarin doka ce kawai, domin an riga an haɗa bashin cikin tsare-tsaren kasafin kuɗi da MTEF tun da farko.

Sanata Sani Musa (Niger Ta Gabas) ya bayyana cewa wannan shiri ba na shekara ɗaya ba ne, amma zai shafi rabon kuɗi na tsawon shekara shida, yana mai jaddada cewa Nijeriya ba ta taɓa gazawa wajen biyan bashinta ba.

Shugaban kwamitin Bankuna da harkokin kuɗi, Sanata Adetokunbo Abiru (Lagos Ta Gabas), ya tabbatar da cewa dukkan bashin na bin ƙa’idojin dokar kula da bashi da ta ɗabi’un da suka dace da dokar kuɗi.

Sai dai Sanata Abdul Ningi (Bauchi Ta Tsakiya) ya nuna damuwa game da ƙarancin bayani da ake da shi kan yadda za a raba bashin da kuma hanyoyin da za a biya su.

Ya nemi a bayyana adadin da kowace jiha ko hukuma za ta samu, da kuma amfanin bashin domin a iya bayyana wa al’umma gaskiya.

A cikin jerin ayyukan da za a aiwatar da kuɗin akwai:

Gina layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri

Tsarin wutar lantarki da sadarwa na zamani

Harkokin tsaro

Noma da aikin gidaje

Sanata Victor Umeh (Anambra Ta Tsakiya) ya goyi bayan shirin, yana mai bayyana cewa wannan ne karon farko da ake ware dala biliyan 3 domin gina layin dogo a gabashin Nijeriya.

Mataimakin Shugaban Majalisa, Barau Jibrin ya yabawa kwamitin bisa aikin da ya yi, yana mai cewa “dukkan yankunan ƙasa na cikin shirin kuma hakan na nuna cewa Agenda ta ‘Renewed Hope’ tana aiki.”

Majalisar ta jaddada cewa duk wani kuɗin da za a fitar dole ne a yi amfani da shi ne kawai wajen ayyukan raya ƙasa da ci gaban al’umma, bisa tanadin dokar kuɗin gwamnati.

Majalisa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya
  • Abubakar Sulaiman
    INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
  • Abubakar Sulaiman
    Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.