Tsohon Ministan Kuɗi da Kula da Tattalin Arziki na ƙasa, Wale Edun, ya miƙa ragamar ofis ga magajinsa, Taiwo Oyedele, wanda shi ne ƙaramin minista a ma’aikatar kuɗi. An gudanar da bikin miƙa ragamar ne a ɓoye ba tare da halartar ‘yan jarida ba.
Hoton bikin miƙa ragamar aikin ya bayyana ne a shafin X na Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya da tsakar dare na ranar Alhamis, 23 ga Afrilu, 2026. Tun da farko dai an gayyaci ‘yan jarida su halarta, amma daga bisani aka sanar da su cewa za a gudanar da bikin a sirri, tare da alƙawarin fitar da sanarwa bayan taron.
Wannan sauyin tsari ya haifar da tambayoyi kan dalilin da ya sa aka gudanar da bikin ba tare da jama’a ko kafafen yaɗa labarai ba. Lamarin ya ƙara jawo hankalin masu sa ido kan harkokin siyasa da tattalin arziƙi.
A gefe guda, an samu raɗe-raɗin cewa an cire minista Edun ne daga muƙaminsa bisa wasu dalilai da suka haɗa da matsalolin lafiya, batutuwan rahoton kasafin kuɗi da kuma buƙatar samun sabon wanda zai fi dacewa da manufofin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.















Discussion about this post