A kwanakin baya-bayan nan dai, yanayin zafi a wasu biranen Indiya ya haura digiri 45 a ma’aunin Celsius. yanayin da ya sanya jama’a a cikin wani hali takura da ya taƙaita wasu harkoki na kaikomo da aka saba domin biya wa kai buƙatu da aka saba.
Yayin da ake fargabar cewa aƙalla mutum 16 ne suka riga mu gidan gaskiya sakamakon tsananin zafin rana a kudancin ƙasar Indiya tun daga farkon bazarar nan zuwa yanzu.
Lamarin ya faru ne a yayin da wata mummunar guguwa mai zafi ke ci gaba da addabar sassa daban-daban a ƙasar da ke kudancin nahiyyar Asiya.
Rahotanni sun ce yanayin zafin ya yi muni musamman a Jihar Telangana, inda gwamnati ta yi kira ga jami’ai su ƙara sanya ido domin kare lafiyar jama’a.
Masana sun ce sauyin yanayi na duniya na ƙara faɗaɗawa da kuma tsananta irin waɗannan guguwar zafi, waɗanda yanzu ke ƙara tsananta fiye da yadda aka saba.
A kwanakin nan dai, yanayin zafi a wasu biranen Indiya ya haura digiri 45 a ma’aunin Celsius, yayin da babban birnin ƙasar, New Delhi, shi ma ke fama da matsanancin zafi fiye da digiri 40 tsawon mako guda.
Ƙwararru a fannin lafiya sun bayyana cewa tsananin zafi kan haddasa bushewar jiki da kaurara jini, lamarin da zai iya jawo gazawar wasu sassan jiki idan ya yi tsanani.
Hukumomi a Telangana sun shawarci tsofaffi da ƙananan yara da mata masu juna biyu da su guji fita a rana sai idan da wata lalura ta tilasta hakan.
Indiya dai na daga cikin ƙasashen da suka fi fitar da hayaƙi mai gurɓata muhalli a duniya, inda har yanzu take dogaro sosai da gawayi ko kuma kwal wajen samar da wutar lantarki.















Discussion about this post