Kwamitin Majalisar Wakilai kan Harkokin Noma da Ayyuka ya fara shirye-shiryen gudanar da bincike kan zargin rashin sakin Naira biliyan 174.26 na kuɗaɗen tallafin noma. Binciken ya biyo bayan ƙudurin da Majalisar ta amince da shi a watan Janairu domin tantance yadda ake aiwatar da shirye-shiryen noma da abokan hulɗar raya ƙasa ke tallafawa.
Shugaban Kwamitin, Hon. Bello Ka’oje, ya buƙaci Ma’aikatun Gwamnati da Hukumomi da Sassan Gwamnati (MDAs) da su gabatar da duk muhimman takardu tare da bayar da cikakken haɗin kai. Ya ce an ɗora wa kwamitin alhakin gano dalilan da suka haddasa jinkirin sakin kuɗaɗen, tare da duba tasirin hakan kan tsadar taki da samar da abinci a ƙasa.
- Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano
- NiMet Ta Yi Hasashen Ruwan Sama Da Wuri, Ta Nemi Manoma Su Jinkirta Shuka
A cewarsa, Nijeriya ta samu rancen dala miliyan 134 daga African Development Bank domin aiwatar da shirin NAGS-AP, inda aka saki dala miliyan 99.67, amma har yanzu Naira biliyan 55.30 da aka ware wa manoma da dillalan kayan noma na noman rani na 2024 da 2025 ba a sake su ba.
Haka kuma, an samu rancen Yen biliyan 15 daga Japan International Cooperation Agency, inda aka saki Yen biliyan 12 (kimanin Naira biliyan 118.96) a watan Maris 2025, amma ba su kai ga hukumomin da za su aiwatar da shirin ba. Kwamitin ya yi gargaɗin cewa jinkirin na iya jefa girbin 2025 da kakar noma ta 2026 cikin haɗari, tare da barazana ga ƙarin tallafin dala miliyan 200 da ake sa ran samu idan ba a aiwatar da shirye-shiryen da suka gabata yadda ya kamata ba.















Discussion about this post