Kusan mutum 620,000 ne suka rasa matsugunansu sakamakon hare-haren ƴan bindiga da satar mutane a yankin Arewa maso Yamma, in ji Hukumar Kula da Ƴan Gudun Hijira ta Duniya (IOM).
Wannan adadi ya kai kusan kashi 84 cikin 100 na mutum 737,073 da aka tabbatar sun rasa matsugunansu a cikin jihohin yankin da hukumar ta gudanar da bincike, a cewar sabon rahoton tantancewar hukumar.
Shugabar Ofishin IOM a Nijeriya, Sharon Dimanche, ce ta bayyana hakan a Katsina yayin wani taron manema labarai kan matsalar raba mutane da matsugunansu da kuma samar da zaman lafiya a Arewa maso Yamma.
Ta ce rashin tsaro shi ne babban abin da ke haddasa raba mutane da matsugunansu a yankin, inda hare-haren ƴan bindiga da satar mutane ke tilasta wa dubban ɗaruruwan mutane barin gidajensu.
Dimanche ta ce Jihar Katsina kaɗai tana da sama da mutum 138,000 da suka rasa matsugunansu sakamakon rashin tsaro da bala’o’in da suka shafi muhalli tsakanin watan Janairun 2025 da Janairun 2026.
Ta ce bala’o’in da suka shafi sauyin yanayi ma na ƙara haddasa matsalar, inda iyalan da abin ya shafa ke rasa hanyoyin samun abin dogaro da kai, tare da fuskantar katsewar karatun yara da kuma tsoro da rashin tabbas.
Shugabar IOM ta ce an samu kusan mutum 147,000 da suka koma gidajensu a faɗin Arewa maso Yamma, ciki har da sama da 37,000 a Jihar Katsina.
A nasa jawabin, Shugaban Reshen IOM na Arewa maso Yamma kuma Manajan Shirye-shirye a Katsina, Jean Nahesi, ya ce haɗin gwiwar hukumar da Tarayyar Turai ta hanyar shirin FPI na taimakawa wajen ƙarfafa ayyukan samar da zaman lafiya, tsarin gargaɗin gaggawa da kuma ƙarfin al’ummomin da abin ya shafa na tinkarar matsaloli.
Nahesi ya yi kira da a ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci, al’umma da abokan hulɗa na ci gaba domin magance tushen matsalar raba mutane da matsugunansu tare da samar da yanayin da zai ba da damar komawa gida cikin aminci da kuma ɗorewa.














