ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansandan Abuja Sun Nemi NLC Ta Dakatar Da Zanga-zangar  Da Ta Shirya Gobe

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC), reshen FCT, da ta yi la’akari tare da sake tsara wa ko dakatar da zanga-zangar lumana da ta shirya gudanarwa a ranar Talata, 3 ga watan Fabrairu, 2026, bisa rahotannin sirri da ke nuna yiwuwar wasu ƙungiyoyi da aka haramta su kutsa cikin zanga-zangar domin tayar da tarzoma.

A wata sanarwa da kakakiyar rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar a ranar Litinin, ta jaddada cewa duk da girmama haƙƙin ’yan ƙasa na taruwa cikin lumana kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada, akwai sahihan bayanan asiri da ke nuna cewa wasu ɓata gari na shirin amfani da damar zanga-zangar domin haddasa rikici.

  • Hukumar FCTA Ta Fatattaki Mabarata 607 Daga Titunan Abuja
  • Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

“Rundunar na girmama haƙƙin taruwa cikin lumana da kundin tsarin mulki ya tanada,” in ji SP Adeh a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na Facebook. “Sai dai rahotannin sirri sun nuna cewa wasu ƙungiyoyi da aka haramta da wasu mutane na shirin kutsa kai ciki su kwace akalar zanga-zangar, wanda hakan na iya barazana ga zaman lafiya da tsaron jama’a.”

ADVERTISEMENT

Ta bayyana cewa an ba da shawarar ga NLC ta sake tsara zanga-zangar ne domin kare lafiyar jama’a da kauce wa yiwuwar taɓarɓarewar doka da oda a babban birnin tarayya.

“Domin kare lafiyar jama’a, Rundunar ’Yansandan FCT ta shawarci masu shirya zanga-zangar da su yi la’akari da sake tsara ta, don hana taɓarɓarewar doka da oda da kuma kare rayuka, da dukiya da haƙƙin sauran mazauna FCT,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

SP Adeh ta kuma tabbatar wa al’umma cewa rundunar na ci gaba da jajircewa wajen kare dukkan ayyukan da doka ta amince da su, tare da kira ga mazauna FCT da su ci gaba da haɗa kai da hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

Ƴansanda
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Tattauna Da Sakataren Hukumar Tsaro Ta Rasha

Wang Yi Ya Tattauna Da Sakataren Hukumar Tsaro Ta Rasha

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.