ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Direba Da Ya Buge Mai PoS Har Lahira Ya Tsere A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Abuja, Nigeria - September 6, 2015: Busy traffic scene on the new built wide highways in outskirts of Nigeria's capital city.

Abuja, Nigeria - September 6, 2015: Busy traffic scene on the new built wide highways in outskirts of Nigeria's capital city.

Wata mata mai sana’ar (POS) ta rasu bayan da wata motar bas ta haya ta buge ta a kusa da gidan mai na Total da ke yankin Berger a Babban Birnin Tarayya (FCT).

Shaidun gani da ido sun ce direban bas din, wanda ke tukin bas ta kasuwa, yana tserewa ne daga jami’an Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) lokacin da lamarin ya faru.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Bayan Jinkiri Da Dimbin Hasashe Abba Kabir Yusuf Ya Rungumi Tafiyar Tinubu

Wani fasinja da lamarin ya faru a gabansa, mai suna Johnson, ya shaida wa wakilinmu cewa matar ta zo aiki da sassafe ta zo tsallaka titi bayan ta sayi abinci. Ya kara da cewa bayan motar bas ta buge ta, ba direban bas din ko jami’an FRSC suka tsaya a wajen ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Matar da aka kashe mai POS ce a yankin. Ta zo da sassafe, ta je ta sayi abinci, tana kokarin tsallaka titi a kusa da gidan mai na Total, sai ga jami’an Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) na bin wata motar coaster bas da gudu. A wannan lokaci, bas din ya buge matar ya jefa ta zuwa daya gefen hanya.”

Ya ci gaba da cewa: “Direban bai tsaya ba. Motar FRSC ma ba ta tsaya ba. Sun ci gaba da bin bas din da gudu sosai. Gawar matar ta jima a kan hanya tare da mummunan rauni. Matar ta rasu kafin jami’an ‘yansanda daga sashen Utako su iso. Wani mutum ya dauki bidiyon duk abin da ya faru ya nuna wa ‘yansanda. Na gan shi yana tafiya tare da su,” in ji Johnson.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Wani mai sayar da jaridu a yankin ya tabbatar da cewa lamarin ya faru da safe a kusa da gidan man Total, yana mai cewa motar bas din da ta buge matar da kuma motar FRSC sun ci gaba da tafiya bayan hadarin.

Wani mai POS a yankin, Ola, ya ce jami’an FRSC suna yawan bin motoci da gudu a yankin. Ya tuna wani makamancin lamari da ya faru a ranar Asabar da ba a samu asarar rai ba saboda karancin jama’a a wancan lokaci.

Ya ce: “A nan ne lamarin ya faru. Jami’an FRSC suna yawan yin irin wannan bin motoci a nan. A ranar Asabar sun bi wata motar coaster bas, a ranar da aka samu cunkoso kamar Litinin, da hakan ya iya kashe wani. Wannan ba shi ne karo na farko da suke bin motoci a wannan wuri ba. Watakila idan muka sake ganinsu a nan, za mu kore su,” in ji shi.

Kwamandan FRSC na FCT, Felid Theman, ya ce hukumar na gudanar da bincike kan lamarin. A cewarsa, an kira dukkan tawagogin sintiri da ke aiki a Central Area, Zone 7, da yankunan da ke makwabtaka domin tantance ko wace motar FRSC ce ta shiga lamarin.

Ya ce: “Na samu rahoto makamancin wannan, kuma a halin yanzu muna bincike. Na kira dukkan tawagogin sintiri, musamman a Central Area, Zone 7 da kewaye, domin gano ko da gaske wata motar sintirinmu ce ta shiga lamarin. Da zarar bincikenmu ya tabbatar da gaskiya, za mu fitar da sanarwa ga manema labarai.”

Ya kara da cewa: “A halin yanzu muna dubawa ne domin tantance sahihancin lamarin. Amma mun san cewa a lokuta da dama, ko da ina amfani da motar aiki kawai, idan wani ya aikata laifi ko ya ketare dokar hanya, mutane kan dauka cewa ana kokarin kama su. Wani lokaci har su kan tare mota, ko da ba a gudanar da sintiri ba.”

Ya ce mutane da yawa ba sa bambance motar sintiri da sauran motoci, yana mai cewa wasu motocin daukar kaya (pickups) ana amfani da su ne don wasu ayyuka daban, ba lallai don sintiri ba.

Ya kammala da cewa: “Har sai mun tabbatar ko da gaske tawagar sintiri ce ke bin wani, zai yi wuri mu ce jami’an sintiri ne ke binsa. Haka kuma na san cewa wannan yanki na da yawan cunkoso sosai.”

Abuja
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
An Cafke Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Mallakar Dakin Sarrafa Miyagun Kwayoyi

An Cafke Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Mallakar Dakin Sarrafa Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.