Wani sabon rikicin cikin gida na kara ta’azzara a jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna, yayin da ake zargin wasu jiga-jigan jam’iyyar da kokarin rage karfin siyasar magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, gabanin zaben shekarar 2027.
Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun shaidawa wakilinmu cewa rikicin ya samo asali ne daga gwagwarmayar neman iko da tikitin gwamna, na majalisar dokoki ta kasa da kuma na majalisar dokokin jihar, inda bangarori daban-daban ke fafatawa domin mallakar tsarin jam’iyyar tun kafin fara zabukan fidda gwani.
Rahotanni sun nuna cewa Salihu Mohammed Lukman na daga cikin fitattun mutanen da ake zargin suna amfani da tasirinsu a matakin kasa wajen tsara makomar siyasar ADC a Kaduna da kuma wadanda za su samu tikitin takara.
Wannan lamari ya haddasa damuwa a bangaren magoya bayan El-Rufai, inda ake zargin cewa ana kokarin mayar da wasu daga cikin amintattunsa saniyar ware duk da rawar da suka taka wajen gina jam’iyyar a jihar.
Daga cikin wadanda ake cewa abin ya shafa akwai tsohon kwamishina Ja’afaru Sani, tsohon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati Bashir Saidu da kuma Hafsat Baba, wadanda ake kallon su a matsayin manyan kusoshin siyasar El-Rufai a Kaduna.
Magoya bayan wannan bangare sun kuma yi nuni da matsalolin shari’a da siyasa da wasu daga cikin kusa da El-Rufai ke fuskanta, musamman Bashir Saidu, a matsayin wata alama da ke nuna cewa ana matsa musu lamba daga ciki da wajen tsarin jam’iyyar.
A gefe guda kuma, wasu majiyoyi sun ce shigowar tsohon dan takarar gwamna na PDP, Isa Ashiru, cikin ADC ya sauya yanayin siyasar jam’iyyar a Kaduna, inda ake zargin wasu masu fada a ji suna son ganin shi ne ya zama zabin jam’iyyar na takarar gwamna a 2027.
Haka kuma ana rade-radin cewa an samu sabani tsakanin Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Lawal Adamu Usman, da Salihu Lukman, yayin da ake zargin akwai wani shiri na sake fasalin tsarin shugabanci da tasirin siyasa a jam’iyyar.
Majiyoyi sun kara da cewa ana yunkurin maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shuaibu Idris Mikati, yayin da ake kuma tunanin maye gurbin Sanata Abdu Kwari da Khalid Soba.
Rikicin ya kara daukar hankali ne bayan da shugabancin ADC na kasa ya dakatar da tsarin zaben cikin gida da ake gudanarwa a Kaduna.
A wata sanarwa da sakataren kwamitin zaben ADC na jihar, Dakta Mohammad Umar, ya fitar, an sanar da ‘yan takara da sauran masu ruwa da tsaki cewa an dakatar da tsarin zaben bisa umarnin sakataren jam’iyyar na kasa har sai an bayar da sabbin umarni.
Wannan mataki ya kara haifar da zargi daga bangaren magoya bayan El-Rufai, wadanda ke ganin cewa ana amfani da shugabancin jam’iyyar na kasa wajen hana su karfafa matsayinsu a cikin ADC tare da bai wa wasu masu iko damar tsara sakamakon zabukan fidda gwani.
Sai dai da yake magana ta wayar tarho, sakataren yada labarai na ADC a Kaduna, Darius Kurah, ya musanta rade-radin da ake yadawa.
Ya ce sabani da fahimtar juna abu ne da ya saba a siyasa, sannan ya musanta cewa akwai wani shiri na maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shu’aibu Idris Mikati.
“A dalilin tabbatar da hadin kai a jam’iyyar ne muka dage zabukan fidda gwani domin bai wa ‘yan takara damar cimma matsaya ta bai daya. Idan hakan bai yiwu ba, za mu koma tsarin zaben kai tsaye,” in ji shi.















Discussion about this post