ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 months ago
ADC

Wani sabon rikicin cikin gida na kara ta’azzara a jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna, yayin da ake zargin wasu jiga-jigan jam’iyyar da kokarin rage karfin siyasar magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, gabanin zaben shekarar 2027.

Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun shaidawa wakilinmu cewa rikicin ya samo asali ne daga gwagwarmayar neman iko da tikitin gwamna, na majalisar dokoki ta kasa da kuma na majalisar dokokin jihar, inda bangarori daban-daban ke fafatawa domin mallakar tsarin jam’iyyar tun kafin fara zabukan fidda gwani.

Rahotanni sun nuna cewa Salihu Mohammed Lukman na daga cikin fitattun mutanen da ake zargin suna amfani da tasirinsu a matakin kasa wajen tsara makomar siyasar ADC a Kaduna da kuma wadanda za su samu tikitin takara.

ADVERTISEMENT

Wannan lamari ya haddasa damuwa a bangaren magoya bayan El-Rufai, inda ake zargin cewa ana kokarin mayar da wasu daga cikin amintattunsa saniyar ware duk da rawar da suka taka wajen gina jam’iyyar a jihar.

Daga cikin wadanda ake cewa abin ya shafa akwai tsohon kwamishina Ja’afaru Sani, tsohon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati Bashir Saidu da kuma Hafsat Baba, wadanda ake kallon su a matsayin manyan kusoshin siyasar El-Rufai a Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Magoya bayan wannan bangare sun kuma yi nuni da matsalolin shari’a da siyasa da wasu daga cikin kusa da El-Rufai ke fuskanta, musamman Bashir Saidu, a matsayin wata alama da ke nuna cewa ana matsa musu lamba daga ciki da wajen tsarin jam’iyyar.

A gefe guda kuma, wasu majiyoyi sun ce shigowar tsohon dan takarar gwamna na PDP, Isa Ashiru, cikin ADC ya sauya yanayin siyasar jam’iyyar a Kaduna, inda ake zargin wasu masu fada a ji suna son ganin shi ne ya zama zabin jam’iyyar na takarar gwamna a 2027.

Haka kuma ana rade-radin cewa an samu sabani tsakanin Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Lawal Adamu Usman, da Salihu Lukman, yayin da ake zargin akwai wani shiri na sake fasalin tsarin shugabanci da tasirin siyasa a jam’iyyar.

Majiyoyi sun kara da cewa ana yunkurin maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shuaibu Idris Mikati, yayin da ake kuma tunanin maye gurbin Sanata Abdu Kwari da Khalid Soba.

Rikicin ya kara daukar hankali ne bayan da shugabancin ADC na kasa ya dakatar da tsarin zaben cikin gida da ake gudanarwa a Kaduna.

A wata sanarwa da sakataren kwamitin zaben ADC na jihar, Dakta Mohammad Umar, ya fitar, an sanar da ‘yan takara da sauran masu ruwa da tsaki cewa an dakatar da tsarin zaben bisa umarnin sakataren jam’iyyar na kasa har sai an bayar da sabbin umarni.

Wannan mataki ya kara haifar da zargi daga bangaren magoya bayan El-Rufai, wadanda ke ganin cewa ana amfani da shugabancin jam’iyyar na kasa wajen hana su karfafa matsayinsu a cikin ADC tare da bai wa wasu masu iko damar tsara sakamakon zabukan fidda gwani.

Sai dai da yake magana ta wayar tarho, sakataren yada labarai na ADC a Kaduna, Darius Kurah, ya musanta rade-radin da ake yadawa.

Ya ce sabani da fahimtar juna abu ne da ya saba a siyasa, sannan ya musanta cewa akwai wani shiri na maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shu’aibu Idris Mikati.

“A dalilin tabbatar da hadin kai a jam’iyyar ne muka dage zabukan fidda gwani domin bai wa ‘yan takara damar cimma matsaya ta bai daya. Idan hakan bai yiwu ba, za mu koma tsarin zaben kai tsaye,” in ji shi.

ADC
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

July 13, 2026
Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

July 13, 2026
Sin Ta Fitar Da Rahoton “Sake Karyata Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

Sin Ta Fitar Da Rahoton “Sake Karyata Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 13, 2026
Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.