ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 weeks ago
ADC

Wani sabon rikicin cikin gida na kara ta’azzara a jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna, yayin da ake zargin wasu jiga-jigan jam’iyyar da kokarin rage karfin siyasar magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, gabanin zaben shekarar 2027.

Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun shaidawa wakilinmu cewa rikicin ya samo asali ne daga gwagwarmayar neman iko da tikitin gwamna, na majalisar dokoki ta kasa da kuma na majalisar dokokin jihar, inda bangarori daban-daban ke fafatawa domin mallakar tsarin jam’iyyar tun kafin fara zabukan fidda gwani.

Rahotanni sun nuna cewa Salihu Mohammed Lukman na daga cikin fitattun mutanen da ake zargin suna amfani da tasirinsu a matakin kasa wajen tsara makomar siyasar ADC a Kaduna da kuma wadanda za su samu tikitin takara.

ADVERTISEMENT

Wannan lamari ya haddasa damuwa a bangaren magoya bayan El-Rufai, inda ake zargin cewa ana kokarin mayar da wasu daga cikin amintattunsa saniyar ware duk da rawar da suka taka wajen gina jam’iyyar a jihar.

Daga cikin wadanda ake cewa abin ya shafa akwai tsohon kwamishina Ja’afaru Sani, tsohon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati Bashir Saidu da kuma Hafsat Baba, wadanda ake kallon su a matsayin manyan kusoshin siyasar El-Rufai a Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Magoya bayan wannan bangare sun kuma yi nuni da matsalolin shari’a da siyasa da wasu daga cikin kusa da El-Rufai ke fuskanta, musamman Bashir Saidu, a matsayin wata alama da ke nuna cewa ana matsa musu lamba daga ciki da wajen tsarin jam’iyyar.

A gefe guda kuma, wasu majiyoyi sun ce shigowar tsohon dan takarar gwamna na PDP, Isa Ashiru, cikin ADC ya sauya yanayin siyasar jam’iyyar a Kaduna, inda ake zargin wasu masu fada a ji suna son ganin shi ne ya zama zabin jam’iyyar na takarar gwamna a 2027.

Haka kuma ana rade-radin cewa an samu sabani tsakanin Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Lawal Adamu Usman, da Salihu Lukman, yayin da ake zargin akwai wani shiri na sake fasalin tsarin shugabanci da tasirin siyasa a jam’iyyar.

Majiyoyi sun kara da cewa ana yunkurin maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shuaibu Idris Mikati, yayin da ake kuma tunanin maye gurbin Sanata Abdu Kwari da Khalid Soba.

Rikicin ya kara daukar hankali ne bayan da shugabancin ADC na kasa ya dakatar da tsarin zaben cikin gida da ake gudanarwa a Kaduna.

A wata sanarwa da sakataren kwamitin zaben ADC na jihar, Dakta Mohammad Umar, ya fitar, an sanar da ‘yan takara da sauran masu ruwa da tsaki cewa an dakatar da tsarin zaben bisa umarnin sakataren jam’iyyar na kasa har sai an bayar da sabbin umarni.

Wannan mataki ya kara haifar da zargi daga bangaren magoya bayan El-Rufai, wadanda ke ganin cewa ana amfani da shugabancin jam’iyyar na kasa wajen hana su karfafa matsayinsu a cikin ADC tare da bai wa wasu masu iko damar tsara sakamakon zabukan fidda gwani.

Sai dai da yake magana ta wayar tarho, sakataren yada labarai na ADC a Kaduna, Darius Kurah, ya musanta rade-radin da ake yadawa.

Ya ce sabani da fahimtar juna abu ne da ya saba a siyasa, sannan ya musanta cewa akwai wani shiri na maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shu’aibu Idris Mikati.

“A dalilin tabbatar da hadin kai a jam’iyyar ne muka dage zabukan fidda gwani domin bai wa ‘yan takara damar cimma matsaya ta bai daya. Idan hakan bai yiwu ba, za mu koma tsarin zaben kai tsaye,” in ji shi.

ADC
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Za Mu Fifita Ayyukan Matasa Idan Muka Samu Gwamnati – Hon. Yazid Atta
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.