ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

by Shehu Yahaya and Sulaiman
1 month ago
ADC

Wani sabon rikicin cikin gida na kara ta’azzara a jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna, yayin da ake zargin wasu jiga-jigan jam’iyyar da kokarin rage karfin siyasar magoya bayan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, gabanin zaben shekarar 2027.

Majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun shaidawa wakilinmu cewa rikicin ya samo asali ne daga gwagwarmayar neman iko da tikitin gwamna, na majalisar dokoki ta kasa da kuma na majalisar dokokin jihar, inda bangarori daban-daban ke fafatawa domin mallakar tsarin jam’iyyar tun kafin fara zabukan fidda gwani.

Rahotanni sun nuna cewa Salihu Mohammed Lukman na daga cikin fitattun mutanen da ake zargin suna amfani da tasirinsu a matakin kasa wajen tsara makomar siyasar ADC a Kaduna da kuma wadanda za su samu tikitin takara.

ADVERTISEMENT

Wannan lamari ya haddasa damuwa a bangaren magoya bayan El-Rufai, inda ake zargin cewa ana kokarin mayar da wasu daga cikin amintattunsa saniyar ware duk da rawar da suka taka wajen gina jam’iyyar a jihar.

Daga cikin wadanda ake cewa abin ya shafa akwai tsohon kwamishina Ja’afaru Sani, tsohon shugaban ma’aikatan gidan gwamnati Bashir Saidu da kuma Hafsat Baba, wadanda ake kallon su a matsayin manyan kusoshin siyasar El-Rufai a Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Magoya bayan wannan bangare sun kuma yi nuni da matsalolin shari’a da siyasa da wasu daga cikin kusa da El-Rufai ke fuskanta, musamman Bashir Saidu, a matsayin wata alama da ke nuna cewa ana matsa musu lamba daga ciki da wajen tsarin jam’iyyar.

A gefe guda kuma, wasu majiyoyi sun ce shigowar tsohon dan takarar gwamna na PDP, Isa Ashiru, cikin ADC ya sauya yanayin siyasar jam’iyyar a Kaduna, inda ake zargin wasu masu fada a ji suna son ganin shi ne ya zama zabin jam’iyyar na takarar gwamna a 2027.

Haka kuma ana rade-radin cewa an samu sabani tsakanin Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Lawal Adamu Usman, da Salihu Lukman, yayin da ake zargin akwai wani shiri na sake fasalin tsarin shugabanci da tasirin siyasa a jam’iyyar.

Majiyoyi sun kara da cewa ana yunkurin maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shuaibu Idris Mikati, yayin da ake kuma tunanin maye gurbin Sanata Abdu Kwari da Khalid Soba.

Rikicin ya kara daukar hankali ne bayan da shugabancin ADC na kasa ya dakatar da tsarin zaben cikin gida da ake gudanarwa a Kaduna.

A wata sanarwa da sakataren kwamitin zaben ADC na jihar, Dakta Mohammad Umar, ya fitar, an sanar da ‘yan takara da sauran masu ruwa da tsaki cewa an dakatar da tsarin zaben bisa umarnin sakataren jam’iyyar na kasa har sai an bayar da sabbin umarni.

Wannan mataki ya kara haifar da zargi daga bangaren magoya bayan El-Rufai, wadanda ke ganin cewa ana amfani da shugabancin jam’iyyar na kasa wajen hana su karfafa matsayinsu a cikin ADC tare da bai wa wasu masu iko damar tsara sakamakon zabukan fidda gwani.

Sai dai da yake magana ta wayar tarho, sakataren yada labarai na ADC a Kaduna, Darius Kurah, ya musanta rade-radin da ake yadawa.

Ya ce sabani da fahimtar juna abu ne da ya saba a siyasa, sannan ya musanta cewa akwai wani shiri na maye gurbin Sanata Lawal Adamu da Shu’aibu Idris Mikati.

“A dalilin tabbatar da hadin kai a jam’iyyar ne muka dage zabukan fidda gwani domin bai wa ‘yan takara damar cimma matsaya ta bai daya. Idan hakan bai yiwu ba, za mu koma tsarin zaben kai tsaye,” in ji shi.

ADC
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Babban Darektan UNESCO

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.