• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Bukaci A Hana Gwamnan Gombe Da Mataimakinsa Takara Kan Zargin Gabatar Da Takardun Bogi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Siyasa
0
2023: PDP Ta Bukaci A Hana Gwamnan Gombe Da Mataimakinsa Takara Kan Zargin Gabatar Da Takardun Bogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta garzaya babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, inda ta  nemi kotun ta hana Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da mataimakinsa Jatau Manassah Daniel, shiga a dama da su a zaben 2023 bisa zarginsu da gabatar da takardun bogi.

A kara mai lamba FJC/ABJ/CS/1301/2022 da ke tsakanin jam’iyyar PDP da wasu mutum biyu (masu kara) da INEC da wasu uku (wadanda ake kara) da aka shigar a ranar 2 ga watan Agustan 2022, PDP na rokon kotun da ta hana gwamna Inuwa da mataimakinsa yin takarar gwamnan jihar Gombe, kan zarginsu da mika takardun bogi ga INEC kuma aka wallafa a ranar 22 ga watan Yulin 2022.

A takardar sammacin da suka shigar ta hannun lauyiyinsu Cif Arthur Obi Okafor, (SAN) da J.J. Usman, (SAN), masu kara sun ce Inuwa da mataimakinsa, sun shigar da bayanai na karya da ake zargin suna amfani da takardun bogi ne.

Don haka ne suka nemi a hana su takarar bisa kafa hujja da cewa irin wannan batun ya saba wa sashe 177(d) da sashe 182(1) (j) na kundin tsarin mulkin kasa na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima).

A takardun kotun da wakilinmu ya samu, masu korafi sun yi zargin cewa, Jatau na amfani da sunayen daban-daban a takardar shaidar kammala Firamare (Manassah Jatau), shaidar kammala Sakandare ta (WAEC) (Daniel Manassah J), shaidar kammala Jami’ar Maiduguri (Manassah Daniel Jatau), shaidar kammala hidimar kasa (NYSC) (Daniel Manassah) ba tare da tantancewa ko hadawa da wata shaidar canja suna a cikin fom din EC-9 da ya mika wa INEC ba.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

Masu gabatar da kara sun yi zargin cewa a 2022 gwamna Inuwa l, ya gabatar da fom dinsa na EC-9 (takardar neman zama gwamnan Jihar Gombe), inda ya ce ya yi aiki a kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1984 da kamfanin A.Y.U & Co.Ltd a tsakanin 1985-2003, sabanin yadda ya ce a 2018 a cewa ya yi aiki da kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1985 da kuma A.Y.U & Co. Ltd a tsakanin 1980-1990.

A cewar masu shigar da karar, mataimakin Inuwa (Jatau), ya makala takardar shaidar bautar kasa mai dauke da kwanan watan 31 ga watan Yuli, 1980, inda ya bayyana haka: “Wannan shi ne don tabbatar da cewa Daniel Manassah NYSC/Mad/79/6201 ya cika shekara guda na hidimar kasa daga ranar 1 ga watan Yuli, Agusta 1979 zuwa 31 ga Yuli 1980 bisa ga sashe na 11 na dokar hidimar matasa ta kasa (NYSC) mai lamba 24 na 1973.

Masu shigar da karar sun ci gaba da cewa, mataimakin gwamnan wanda ya yi ikirarin ya yi aiki da sojan Nijeriya tun daga watan Agustan 1979 zuwa Yuli 1980, ya mika takardar shaidar kammala NYSC, wanda ya nuna cewa ya fara yin hidimar kasa a watan Agustan 1979 kuma ya kammala, haka a watan Yuli 1979.

Masu karar sun kuma kara da cewa daga sakin layi D na Fom din EC-9 da Jatau ya gabatar wa INEC, ya yi ikirarin cewa ya yi aiki da rundunar soji daga watan Yulin 1979 zuwa watan Agustan 1980 kuma dalilinsa na barin aikin soja din a watan Yulin 1980.

Sun kara da cewa, Jatau ya ce ya fara hidimar kasa bayan da bar aikin soja a watan Yulin 1980 amma ya gabatar wa INEC shaidar NYSC da ke cewa ya fara hidimar kasa daga watan Agustan 1979 zuwa watan Yulin 1979 (ya kammala).

Masu karar sai suka hakikance kan cewa Fom din rantsuwa ta EC-9 da gwamna Inuwa da mataimakinsa Jatau suka gabatar akwai bayanai na karya da dama a ciki ko kuma sun gabatar da takardun bogi don haka ba su cancanci shiga takarar siyasa ba.

Masu shigar da karar sun roki kotun ta gaggauta tsaida Inuwa da Jatau daga shiga a dama da su a neman kujerar gwamnan Jihar Gombe a 2023.

Sai dai kotu ba ta sanya ranar fara sauraron karar ba zuwa yanzu.

Tags: GombeInuwa MohammedJatauKotuNYSCPDPSiyasaTakardun BogiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Tsaro: Majalisa Ta Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Next Post

NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 

Related

Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)
Manyan Labarai

PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

3 days ago
Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

4 days ago
Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)
Manyan Labarai

Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)

4 days ago
NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara
Siyasa

NNPP Ta Kai Korafinta Ga Hukumar NJC Kan Kalaman Daya Da Cikin Alkalan Kotun Zaben Kano

5 days ago
Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin
Manyan Labarai

Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin

1 week ago
Shari’ar Zaben Gwamnan Bauchi: Sai Mun Ga Abin Da Ya Ture Wa Buzu Nadi – Dan Takarar APC
Siyasa

Shari’ar Zaben Gwamnan Bauchi: Sai Mun Ga Abin Da Ya Ture Wa Buzu Nadi – Dan Takarar APC

1 week ago
Next Post
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 

NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan 'Yan Bindiga 

LABARAI MASU NASABA

Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.