ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Bukaci A Hana Gwamnan Gombe Da Mataimakinsa Takara Kan Zargin Gabatar Da Takardun Bogi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta garzaya babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, inda ta  nemi kotun ta hana Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da mataimakinsa Jatau Manassah Daniel, shiga a dama da su a zaben 2023 bisa zarginsu da gabatar da takardun bogi.

A kara mai lamba FJC/ABJ/CS/1301/2022 da ke tsakanin jam’iyyar PDP da wasu mutum biyu (masu kara) da INEC da wasu uku (wadanda ake kara) da aka shigar a ranar 2 ga watan Agustan 2022, PDP na rokon kotun da ta hana gwamna Inuwa da mataimakinsa yin takarar gwamnan jihar Gombe, kan zarginsu da mika takardun bogi ga INEC kuma aka wallafa a ranar 22 ga watan Yulin 2022.

A takardar sammacin da suka shigar ta hannun lauyiyinsu Cif Arthur Obi Okafor, (SAN) da J.J. Usman, (SAN), masu kara sun ce Inuwa da mataimakinsa, sun shigar da bayanai na karya da ake zargin suna amfani da takardun bogi ne.

ADVERTISEMENT

Don haka ne suka nemi a hana su takarar bisa kafa hujja da cewa irin wannan batun ya saba wa sashe 177(d) da sashe 182(1) (j) na kundin tsarin mulkin kasa na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima).

A takardun kotun da wakilinmu ya samu, masu korafi sun yi zargin cewa, Jatau na amfani da sunayen daban-daban a takardar shaidar kammala Firamare (Manassah Jatau), shaidar kammala Sakandare ta (WAEC) (Daniel Manassah J), shaidar kammala Jami’ar Maiduguri (Manassah Daniel Jatau), shaidar kammala hidimar kasa (NYSC) (Daniel Manassah) ba tare da tantancewa ko hadawa da wata shaidar canja suna a cikin fom din EC-9 da ya mika wa INEC ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Masu gabatar da kara sun yi zargin cewa a 2022 gwamna Inuwa l, ya gabatar da fom dinsa na EC-9 (takardar neman zama gwamnan Jihar Gombe), inda ya ce ya yi aiki a kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1984 da kamfanin A.Y.U & Co.Ltd a tsakanin 1985-2003, sabanin yadda ya ce a 2018 a cewa ya yi aiki da kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1985 da kuma A.Y.U & Co. Ltd a tsakanin 1980-1990.

A cewar masu shigar da karar, mataimakin Inuwa (Jatau), ya makala takardar shaidar bautar kasa mai dauke da kwanan watan 31 ga watan Yuli, 1980, inda ya bayyana haka: “Wannan shi ne don tabbatar da cewa Daniel Manassah NYSC/Mad/79/6201 ya cika shekara guda na hidimar kasa daga ranar 1 ga watan Yuli, Agusta 1979 zuwa 31 ga Yuli 1980 bisa ga sashe na 11 na dokar hidimar matasa ta kasa (NYSC) mai lamba 24 na 1973.

Masu shigar da karar sun ci gaba da cewa, mataimakin gwamnan wanda ya yi ikirarin ya yi aiki da sojan Nijeriya tun daga watan Agustan 1979 zuwa Yuli 1980, ya mika takardar shaidar kammala NYSC, wanda ya nuna cewa ya fara yin hidimar kasa a watan Agustan 1979 kuma ya kammala, haka a watan Yuli 1979.

Masu karar sun kuma kara da cewa daga sakin layi D na Fom din EC-9 da Jatau ya gabatar wa INEC, ya yi ikirarin cewa ya yi aiki da rundunar soji daga watan Yulin 1979 zuwa watan Agustan 1980 kuma dalilinsa na barin aikin soja din a watan Yulin 1980.

Sun kara da cewa, Jatau ya ce ya fara hidimar kasa bayan da bar aikin soja a watan Yulin 1980 amma ya gabatar wa INEC shaidar NYSC da ke cewa ya fara hidimar kasa daga watan Agustan 1979 zuwa watan Yulin 1979 (ya kammala).

Masu karar sai suka hakikance kan cewa Fom din rantsuwa ta EC-9 da gwamna Inuwa da mataimakinsa Jatau suka gabatar akwai bayanai na karya da dama a ciki ko kuma sun gabatar da takardun bogi don haka ba su cancanci shiga takarar siyasa ba.

Masu shigar da karar sun roki kotun ta gaggauta tsaida Inuwa da Jatau daga shiga a dama da su a neman kujerar gwamnan Jihar Gombe a 2023.

Sai dai kotu ba ta sanya ranar fara sauraron karar ba zuwa yanzu.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 

NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan 'Yan Bindiga 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.