ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Bukaci A Hana Gwamnan Gombe Da Mataimakinsa Takara Kan Zargin Gabatar Da Takardun Bogi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta garzaya babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, inda ta  nemi kotun ta hana Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da mataimakinsa Jatau Manassah Daniel, shiga a dama da su a zaben 2023 bisa zarginsu da gabatar da takardun bogi.

A kara mai lamba FJC/ABJ/CS/1301/2022 da ke tsakanin jam’iyyar PDP da wasu mutum biyu (masu kara) da INEC da wasu uku (wadanda ake kara) da aka shigar a ranar 2 ga watan Agustan 2022, PDP na rokon kotun da ta hana gwamna Inuwa da mataimakinsa yin takarar gwamnan jihar Gombe, kan zarginsu da mika takardun bogi ga INEC kuma aka wallafa a ranar 22 ga watan Yulin 2022.

A takardar sammacin da suka shigar ta hannun lauyiyinsu Cif Arthur Obi Okafor, (SAN) da J.J. Usman, (SAN), masu kara sun ce Inuwa da mataimakinsa, sun shigar da bayanai na karya da ake zargin suna amfani da takardun bogi ne.

ADVERTISEMENT

Don haka ne suka nemi a hana su takarar bisa kafa hujja da cewa irin wannan batun ya saba wa sashe 177(d) da sashe 182(1) (j) na kundin tsarin mulkin kasa na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima).

A takardun kotun da wakilinmu ya samu, masu korafi sun yi zargin cewa, Jatau na amfani da sunayen daban-daban a takardar shaidar kammala Firamare (Manassah Jatau), shaidar kammala Sakandare ta (WAEC) (Daniel Manassah J), shaidar kammala Jami’ar Maiduguri (Manassah Daniel Jatau), shaidar kammala hidimar kasa (NYSC) (Daniel Manassah) ba tare da tantancewa ko hadawa da wata shaidar canja suna a cikin fom din EC-9 da ya mika wa INEC ba.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Masu gabatar da kara sun yi zargin cewa a 2022 gwamna Inuwa l, ya gabatar da fom dinsa na EC-9 (takardar neman zama gwamnan Jihar Gombe), inda ya ce ya yi aiki a kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1984 da kamfanin A.Y.U & Co.Ltd a tsakanin 1985-2003, sabanin yadda ya ce a 2018 a cewa ya yi aiki da kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1985 da kuma A.Y.U & Co. Ltd a tsakanin 1980-1990.

A cewar masu shigar da karar, mataimakin Inuwa (Jatau), ya makala takardar shaidar bautar kasa mai dauke da kwanan watan 31 ga watan Yuli, 1980, inda ya bayyana haka: “Wannan shi ne don tabbatar da cewa Daniel Manassah NYSC/Mad/79/6201 ya cika shekara guda na hidimar kasa daga ranar 1 ga watan Yuli, Agusta 1979 zuwa 31 ga Yuli 1980 bisa ga sashe na 11 na dokar hidimar matasa ta kasa (NYSC) mai lamba 24 na 1973.

Masu shigar da karar sun ci gaba da cewa, mataimakin gwamnan wanda ya yi ikirarin ya yi aiki da sojan Nijeriya tun daga watan Agustan 1979 zuwa Yuli 1980, ya mika takardar shaidar kammala NYSC, wanda ya nuna cewa ya fara yin hidimar kasa a watan Agustan 1979 kuma ya kammala, haka a watan Yuli 1979.

Masu karar sun kuma kara da cewa daga sakin layi D na Fom din EC-9 da Jatau ya gabatar wa INEC, ya yi ikirarin cewa ya yi aiki da rundunar soji daga watan Yulin 1979 zuwa watan Agustan 1980 kuma dalilinsa na barin aikin soja din a watan Yulin 1980.

Sun kara da cewa, Jatau ya ce ya fara hidimar kasa bayan da bar aikin soja a watan Yulin 1980 amma ya gabatar wa INEC shaidar NYSC da ke cewa ya fara hidimar kasa daga watan Agustan 1979 zuwa watan Yulin 1979 (ya kammala).

Masu karar sai suka hakikance kan cewa Fom din rantsuwa ta EC-9 da gwamna Inuwa da mataimakinsa Jatau suka gabatar akwai bayanai na karya da dama a ciki ko kuma sun gabatar da takardun bogi don haka ba su cancanci shiga takarar siyasa ba.

Masu shigar da karar sun roki kotun ta gaggauta tsaida Inuwa da Jatau daga shiga a dama da su a neman kujerar gwamnan Jihar Gombe a 2023.

Sai dai kotu ba ta sanya ranar fara sauraron karar ba zuwa yanzu.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 

NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan 'Yan Bindiga 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.