ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Bukaci A Hana Gwamnan Gombe Da Mataimakinsa Takara Kan Zargin Gabatar Da Takardun Bogi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta garzaya babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, inda ta  nemi kotun ta hana Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da mataimakinsa Jatau Manassah Daniel, shiga a dama da su a zaben 2023 bisa zarginsu da gabatar da takardun bogi.

A kara mai lamba FJC/ABJ/CS/1301/2022 da ke tsakanin jam’iyyar PDP da wasu mutum biyu (masu kara) da INEC da wasu uku (wadanda ake kara) da aka shigar a ranar 2 ga watan Agustan 2022, PDP na rokon kotun da ta hana gwamna Inuwa da mataimakinsa yin takarar gwamnan jihar Gombe, kan zarginsu da mika takardun bogi ga INEC kuma aka wallafa a ranar 22 ga watan Yulin 2022.

A takardar sammacin da suka shigar ta hannun lauyiyinsu Cif Arthur Obi Okafor, (SAN) da J.J. Usman, (SAN), masu kara sun ce Inuwa da mataimakinsa, sun shigar da bayanai na karya da ake zargin suna amfani da takardun bogi ne.

ADVERTISEMENT

Don haka ne suka nemi a hana su takarar bisa kafa hujja da cewa irin wannan batun ya saba wa sashe 177(d) da sashe 182(1) (j) na kundin tsarin mulkin kasa na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima).

A takardun kotun da wakilinmu ya samu, masu korafi sun yi zargin cewa, Jatau na amfani da sunayen daban-daban a takardar shaidar kammala Firamare (Manassah Jatau), shaidar kammala Sakandare ta (WAEC) (Daniel Manassah J), shaidar kammala Jami’ar Maiduguri (Manassah Daniel Jatau), shaidar kammala hidimar kasa (NYSC) (Daniel Manassah) ba tare da tantancewa ko hadawa da wata shaidar canja suna a cikin fom din EC-9 da ya mika wa INEC ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Masu gabatar da kara sun yi zargin cewa a 2022 gwamna Inuwa l, ya gabatar da fom dinsa na EC-9 (takardar neman zama gwamnan Jihar Gombe), inda ya ce ya yi aiki a kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1984 da kamfanin A.Y.U & Co.Ltd a tsakanin 1985-2003, sabanin yadda ya ce a 2018 a cewa ya yi aiki da kamfanin zuba jari na jihar Bauchi a 1985 da kuma A.Y.U & Co. Ltd a tsakanin 1980-1990.

A cewar masu shigar da karar, mataimakin Inuwa (Jatau), ya makala takardar shaidar bautar kasa mai dauke da kwanan watan 31 ga watan Yuli, 1980, inda ya bayyana haka: “Wannan shi ne don tabbatar da cewa Daniel Manassah NYSC/Mad/79/6201 ya cika shekara guda na hidimar kasa daga ranar 1 ga watan Yuli, Agusta 1979 zuwa 31 ga Yuli 1980 bisa ga sashe na 11 na dokar hidimar matasa ta kasa (NYSC) mai lamba 24 na 1973.

Masu shigar da karar sun ci gaba da cewa, mataimakin gwamnan wanda ya yi ikirarin ya yi aiki da sojan Nijeriya tun daga watan Agustan 1979 zuwa Yuli 1980, ya mika takardar shaidar kammala NYSC, wanda ya nuna cewa ya fara yin hidimar kasa a watan Agustan 1979 kuma ya kammala, haka a watan Yuli 1979.

Masu karar sun kuma kara da cewa daga sakin layi D na Fom din EC-9 da Jatau ya gabatar wa INEC, ya yi ikirarin cewa ya yi aiki da rundunar soji daga watan Yulin 1979 zuwa watan Agustan 1980 kuma dalilinsa na barin aikin soja din a watan Yulin 1980.

Sun kara da cewa, Jatau ya ce ya fara hidimar kasa bayan da bar aikin soja a watan Yulin 1980 amma ya gabatar wa INEC shaidar NYSC da ke cewa ya fara hidimar kasa daga watan Agustan 1979 zuwa watan Yulin 1979 (ya kammala).

Masu karar sai suka hakikance kan cewa Fom din rantsuwa ta EC-9 da gwamna Inuwa da mataimakinsa Jatau suka gabatar akwai bayanai na karya da dama a ciki ko kuma sun gabatar da takardun bogi don haka ba su cancanci shiga takarar siyasa ba.

Masu shigar da karar sun roki kotun ta gaggauta tsaida Inuwa da Jatau daga shiga a dama da su a neman kujerar gwamnan Jihar Gombe a 2023.

Sai dai kotu ba ta sanya ranar fara sauraron karar ba zuwa yanzu.

PDP
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
PDP
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 

NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan 'Yan Bindiga 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.