Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya nesanta kansa daga kalaman da ke yawo a kafafen yaɗa labarai dangane da burinsa na siyasa a zaɓen 2027, yana mai cewa ba shi ne ya bayyana su ba.
A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar, El-Rufai ya bayyana cewa maganganun da aka jingina ga wani da ake kira abokinsa a siyasa ba su wakiltar ra’ayinsa.
Bangaren Ilimi A Nijeriya Ya Tabarbare —Uwargidan El-Rufa’i
Rikicin Cikin Gida: ADC DA PRP An Fara Zawarci
Sanarwar ta jaddada cewa El-Rufai ya saba bayyana ra’ayinsa kai tsaye a duk tsawon rayuwarsa ta siyasa, kuma ba zai bai wa wasu damar yin magana a madadinsa ba kan irin waɗannan muhimman batutuwa.
“Haka zalika, duk wata sanarwa da ta shafe shi za ta fito ne kai tsaye daga gare shi ko kuma ta hannun masu magana da yawunsa da aka amince da su,” in ji sanarwar.
Rahotanni sun kuma nuna cewa ana tuhumar El-Rufai a gaban kotuna daban-daban a jihar Kaduna kan zarge-zargen rashawa, inda aka bayar da shi beli kan kuɗi har Naira miliyan 200.















Discussion about this post