Tsohon shugaban ƙasan Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya buƙaci sabon shugaban jam’iyyar PDP, Kabiru Turaki, da ya sake gina jam’iyyar ta hanyar gyara kurakuran da aka yi a baya kuma ya samar da daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.
IBB ya ba da wannan shawarar ne lokacin da Turaki da wasu zaɓaɓɓun mambobin kwamitin zartarwa na PDP suka kai masa ziyara a gidansa na Hilltop da ke garin Minna, babban birnin Jihar Neja.
- Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
- Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Rahotanni sun bayyana cewa a ganawar sun tattaunawa kan sabunta jam’iyyar da samar da daidaino da kwanciyar hankali da buƙatar ƙarfafa tsare-tsaren siyasa a faɗin ƙasar nan.
Tsohon shugaban sojan ya yaba wa shugabancin jam’iyya saboda ta yi daidaito da tsarin gwamnati da mutanen Jihar Neja a lokacin da ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin lokuta mafi wahala tare da sake tabbatar da ƙarfin jam’iyyar PDP a ƙasa nan.
A cewarsa, PDP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi ƙarfi a tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya, ya tuna irin ƙoƙarin da ya yi a baya na kafa tsarin jam’iyyu biyu, wanda ƴan siyasa suka ƙi yarda da shi.
Babangida ya yi kira ga Turaki da ya fifita dabara, yin shawara da shugabanci mai ratsa kowa yayin da yake fara sake gina jam’iyyar.
“Yayin da kake magana a baya, ka amince cewa jam’iyyar ta yi kuskure kuma ta riga ta ƙaddamar da hanyoyi don gyara su. Ina roƙonka ka yi amfani da hikima, ka nemi ra’ayoyin mutane, kuma ka yi aiki wajen gina jam’iyya da samar da zaman lafiya da ci gaba. Kana da ƙarfin yin hakan, kuma ina maka fatan alheri,” in ji shi.
Don nuna tsawon tasirin tsarin jam’iyyu a Nijeriya, tsohon shugaban ƙasa ya bayar da labari game da wani jami’in soja da ya taɓa naɗawa a Jihar Nija, wanda bai san cewa gwamnatin soja ya amshe mulkin Nijeriya ba, kuma ya nace cewa yana biyayya ga shugaba Shehu Shagari da jam’iyyar NPN mai mulki a lokacin ba. Babangida ya ce lamarin ya nuna yadda jam’iyyun siyasa suke matuƙar ɗauke hankalin al’umma.
A cikin jawabinsa, Turaki ya nuna godiya ga kyakkyawar niyya da jagoranci na Babangida, yana cewa PDP za ta ci gaba da amfana da ƙwarewarsa na jagoranci da fahimtarsa ta tarihi kan ci gaban siyasar Nijeriya.
“Mun himmatu wajen sake gyara wannan jam’iyya da sake haɗe dukkan ɓagarorinta wuri ɗaya da dawo da ruhun jam’iyyar domin samun nasara kafin zaɓen 2027,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa tawagar ta shirya wannan ziyara ta musamman don nuna godiya ga Babangida da kuma yin jaje kan garkuwa da mutae da aka yi kwanan nan a Jihar Neja ya sa ya zama dole a haɗe ziyarar da yin ta’aziyya.














