ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: IBB Ya Bai Wa Shugaban PDP Satar Amsar Yadda Zai Jagoranci Jam’iyyar Har Ya Yi Nasara

by Leadership Hausa
7 months ago
Ibb

Tsohon shugaban ƙasan Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya buƙaci sabon shugaban jam’iyyar PDP, Kabiru Turaki, da ya sake gina jam’iyyar ta hanyar gyara kurakuran da aka yi a baya kuma ya samar da daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

IBB ya ba da wannan shawarar ne lokacin da Turaki da wasu zaɓaɓɓun mambobin kwamitin zartarwa na PDP suka kai masa ziyara a gidansa na Hilltop da ke garin Minna, babban birnin Jihar Neja.

  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Rahotanni sun bayyana cewa a ganawar sun tattaunawa kan sabunta jam’iyyar da samar da daidaino da kwanciyar hankali da buƙatar ƙarfafa tsare-tsaren siyasa a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Tsohon shugaban sojan ya yaba wa shugabancin jam’iyya saboda ta yi daidaito da tsarin gwamnati da mutanen Jihar Neja a lokacin da ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin lokuta mafi wahala tare da sake tabbatar da ƙarfin jam’iyyar PDP a ƙasa nan.

A cewarsa, PDP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi ƙarfi a tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya, ya tuna irin ƙoƙarin da ya yi a baya na kafa tsarin jam’iyyu biyu, wanda ƴan siyasa suka ƙi yarda da shi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Babangida ya yi kira ga Turaki da ya fifita dabara, yin shawara da shugabanci mai ratsa kowa yayin da yake fara sake gina jam’iyyar.

“Yayin da kake magana a baya, ka amince cewa jam’iyyar ta yi kuskure kuma ta riga ta ƙaddamar da hanyoyi don gyara su. Ina roƙonka ka yi amfani da hikima, ka nemi ra’ayoyin mutane, kuma ka yi aiki wajen gina jam’iyya da samar da zaman lafiya da ci gaba. Kana da ƙarfin yin hakan, kuma ina maka fatan alheri,” in ji shi.

Don nuna tsawon tasirin tsarin jam’iyyu a Nijeriya, tsohon shugaban ƙasa ya bayar da labari game da wani jami’in soja da ya taɓa naɗawa a Jihar Nija, wanda bai san cewa gwamnatin soja ya amshe mulkin Nijeriya ba, kuma ya nace cewa yana biyayya ga shugaba Shehu Shagari da jam’iyyar NPN mai mulki a lokacin ba. Babangida ya ce lamarin ya nuna yadda jam’iyyun siyasa suke matuƙar ɗauke hankalin al’umma.

A cikin jawabinsa, Turaki ya nuna godiya ga kyakkyawar niyya da jagoranci na Babangida, yana cewa PDP za ta ci gaba da amfana da ƙwarewarsa na jagoranci da fahimtarsa ta tarihi kan ci gaban siyasar Nijeriya.

“Mun himmatu wajen sake gyara wannan jam’iyya da sake haɗe dukkan ɓagarorinta wuri ɗaya da dawo da ruhun jam’iyyar domin samun nasara kafin zaɓen 2027,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa tawagar ta shirya wannan ziyara ta musamman don nuna godiya ga Babangida da kuma yin jaje kan garkuwa da mutae da aka yi kwanan nan a Jihar Neja ya sa ya zama dole a haɗe ziyarar da yin ta’aziyya.

Ibb
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.