ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: IBB Ya Bai Wa Shugaban PDP Satar Amsar Yadda Zai Jagoranci Jam’iyyar Har Ya Yi Nasara

by Leadership Hausa
6 months ago
Ibb

Tsohon shugaban ƙasan Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya buƙaci sabon shugaban jam’iyyar PDP, Kabiru Turaki, da ya sake gina jam’iyyar ta hanyar gyara kurakuran da aka yi a baya kuma ya samar da daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

IBB ya ba da wannan shawarar ne lokacin da Turaki da wasu zaɓaɓɓun mambobin kwamitin zartarwa na PDP suka kai masa ziyara a gidansa na Hilltop da ke garin Minna, babban birnin Jihar Neja.

  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Rahotanni sun bayyana cewa a ganawar sun tattaunawa kan sabunta jam’iyyar da samar da daidaino da kwanciyar hankali da buƙatar ƙarfafa tsare-tsaren siyasa a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Tsohon shugaban sojan ya yaba wa shugabancin jam’iyya saboda ta yi daidaito da tsarin gwamnati da mutanen Jihar Neja a lokacin da ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin lokuta mafi wahala tare da sake tabbatar da ƙarfin jam’iyyar PDP a ƙasa nan.

A cewarsa, PDP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi ƙarfi a tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya, ya tuna irin ƙoƙarin da ya yi a baya na kafa tsarin jam’iyyu biyu, wanda ƴan siyasa suka ƙi yarda da shi.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Babangida ya yi kira ga Turaki da ya fifita dabara, yin shawara da shugabanci mai ratsa kowa yayin da yake fara sake gina jam’iyyar.

“Yayin da kake magana a baya, ka amince cewa jam’iyyar ta yi kuskure kuma ta riga ta ƙaddamar da hanyoyi don gyara su. Ina roƙonka ka yi amfani da hikima, ka nemi ra’ayoyin mutane, kuma ka yi aiki wajen gina jam’iyya da samar da zaman lafiya da ci gaba. Kana da ƙarfin yin hakan, kuma ina maka fatan alheri,” in ji shi.

Don nuna tsawon tasirin tsarin jam’iyyu a Nijeriya, tsohon shugaban ƙasa ya bayar da labari game da wani jami’in soja da ya taɓa naɗawa a Jihar Nija, wanda bai san cewa gwamnatin soja ya amshe mulkin Nijeriya ba, kuma ya nace cewa yana biyayya ga shugaba Shehu Shagari da jam’iyyar NPN mai mulki a lokacin ba. Babangida ya ce lamarin ya nuna yadda jam’iyyun siyasa suke matuƙar ɗauke hankalin al’umma.

A cikin jawabinsa, Turaki ya nuna godiya ga kyakkyawar niyya da jagoranci na Babangida, yana cewa PDP za ta ci gaba da amfana da ƙwarewarsa na jagoranci da fahimtarsa ta tarihi kan ci gaban siyasar Nijeriya.

“Mun himmatu wajen sake gyara wannan jam’iyya da sake haɗe dukkan ɓagarorinta wuri ɗaya da dawo da ruhun jam’iyyar domin samun nasara kafin zaɓen 2027,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa tawagar ta shirya wannan ziyara ta musamman don nuna godiya ga Babangida da kuma yin jaje kan garkuwa da mutae da aka yi kwanan nan a Jihar Neja ya sa ya zama dole a haɗe ziyarar da yin ta’aziyya.

Ibb
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.