ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: IBB Ya Bai Wa Shugaban PDP Satar Amsar Yadda Zai Jagoranci Jam’iyyar Har Ya Yi Nasara

by Leadership Hausa
7 months ago
Ibb

Tsohon shugaban ƙasan Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya buƙaci sabon shugaban jam’iyyar PDP, Kabiru Turaki, da ya sake gina jam’iyyar ta hanyar gyara kurakuran da aka yi a baya kuma ya samar da daidaito a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

IBB ya ba da wannan shawarar ne lokacin da Turaki da wasu zaɓaɓɓun mambobin kwamitin zartarwa na PDP suka kai masa ziyara a gidansa na Hilltop da ke garin Minna, babban birnin Jihar Neja.

  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Rahotanni sun bayyana cewa a ganawar sun tattaunawa kan sabunta jam’iyyar da samar da daidaino da kwanciyar hankali da buƙatar ƙarfafa tsare-tsaren siyasa a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Tsohon shugaban sojan ya yaba wa shugabancin jam’iyya saboda ta yi daidaito da tsarin gwamnati da mutanen Jihar Neja a lokacin da ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin lokuta mafi wahala tare da sake tabbatar da ƙarfin jam’iyyar PDP a ƙasa nan.

A cewarsa, PDP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi ƙarfi a tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya, ya tuna irin ƙoƙarin da ya yi a baya na kafa tsarin jam’iyyu biyu, wanda ƴan siyasa suka ƙi yarda da shi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Babangida ya yi kira ga Turaki da ya fifita dabara, yin shawara da shugabanci mai ratsa kowa yayin da yake fara sake gina jam’iyyar.

“Yayin da kake magana a baya, ka amince cewa jam’iyyar ta yi kuskure kuma ta riga ta ƙaddamar da hanyoyi don gyara su. Ina roƙonka ka yi amfani da hikima, ka nemi ra’ayoyin mutane, kuma ka yi aiki wajen gina jam’iyya da samar da zaman lafiya da ci gaba. Kana da ƙarfin yin hakan, kuma ina maka fatan alheri,” in ji shi.

Don nuna tsawon tasirin tsarin jam’iyyu a Nijeriya, tsohon shugaban ƙasa ya bayar da labari game da wani jami’in soja da ya taɓa naɗawa a Jihar Nija, wanda bai san cewa gwamnatin soja ya amshe mulkin Nijeriya ba, kuma ya nace cewa yana biyayya ga shugaba Shehu Shagari da jam’iyyar NPN mai mulki a lokacin ba. Babangida ya ce lamarin ya nuna yadda jam’iyyun siyasa suke matuƙar ɗauke hankalin al’umma.

A cikin jawabinsa, Turaki ya nuna godiya ga kyakkyawar niyya da jagoranci na Babangida, yana cewa PDP za ta ci gaba da amfana da ƙwarewarsa na jagoranci da fahimtarsa ta tarihi kan ci gaban siyasar Nijeriya.

“Mun himmatu wajen sake gyara wannan jam’iyya da sake haɗe dukkan ɓagarorinta wuri ɗaya da dawo da ruhun jam’iyyar domin samun nasara kafin zaɓen 2027,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa tawagar ta shirya wannan ziyara ta musamman don nuna godiya ga Babangida da kuma yin jaje kan garkuwa da mutae da aka yi kwanan nan a Jihar Neja ya sa ya zama dole a haɗe ziyarar da yin ta’aziyya.

Ibb
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.