Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama wata mata da ake zargi da haɗa kai da mayaƙan Boko Haram/ISWAP a wani shingen binciken tsaro da ke ƙaramar hukumar Kukawa.
Masani kan yaƙi da ta’addanci, Zagazola Makama, ya ce matar mai suna Kellu Abba mai shekaru 50 an kama ta ne da misalin ƙarfe 8 na safe ranar Laraba yayin da ake zargin tana kai kayayyaki zuwa wani yanki da mayaƙa ke amfani da shi.
Rahoton ya ce matar, wadda ‘yar ƙabilar Kanuri ce daga yankin Lawanti a garin Baga, tana ƙoƙarin kai kayayyakin ne ga ɗanta mai suna Modu Mustapha wanda ake zargin yana aiki tare da ‘yan ta’adda a yankin Dumba.
Jami’an tsaro sun ce sun ƙwato wasu kayayyaki daga hannunta ciki har da fakiti huɗu na abincin tallafi da aka shirya amfani da su kai tsaye, da hijabai biyu da kuma agogon hannu guda ɗaya. An kuma bayyana cewa a yanzu tana hannun Bataliyar ta 196 domin ci gaba da bincike da yiwuwar gurfanar da ita a kotu.
Dakarun Operation Haɗin Kai sun ce duk da cewa yankin na cikin kwanciyar hankali a halin yanzu, akwai buƙatar ci gaba da sanya ido saboda yanayin tsaron na iya sauyawa a kowane lokaci.















Discussion about this post