Aƙalla mutane 11 sun mutu, yayin da wasu biyu suka jikkata sakamakon harin ‘yan bindiga a ƙauyen Gurbi da ke ƙaramar hukumar Kankara a jihar Katsina.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na Ƴansandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya fitar, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 2:40 na rana a ranar 26 ga Afrilu, 2026, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka mamaye ƙauyen tare da buɗe wuta kan mazauna yankin.
Rundunar ta ce maharan sun kashe mutane 11 tare da jikkata wasu biyu kafin su tsere bayan zuwan jami’an tsaro. An bayyana cewa haɗaɗɗiyar rundunar jami’an tsaro, ciki har da ‘yansanda da sojoji, sun isa wurin cikin gaggawa bayan samun kiran neman taimako.
‘Yansanda sun ƙara da cewa an dawo da zaman lafiya a yankin, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin jinya. Haka kuma, an miƙa gawarwakin waɗanda suka rasu ga iyalansu domin binne su bisa tsarin addinin Musulunci.
Kwamishinan ‘yansanda na jihar, CP Ali Umar Fage, ya tura ƙarin jami’an tsaro domin hana sake faruwar irin wannan hari, tare da umartar ƙara ƙaimi wajen sintiri da tattara bayanan sirri. Rundunar ta jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da farautar waɗanda suka aikata harin domin gurfanar da su a gaban doka.















Discussion about this post