Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi ta Tarayya, ta gargadi masu kiwon kiwon kajin gidan gona da ke kasar nan, da su sanya ido sosai, kan yiwuwar bullar cutar murar tsintsaye (Bird Flu).
Wannan gargadin na zuwa ne, domin daukar matakai, biyo bayan bullar mummunar cutar murar tsintsaye a Kasar Amurka da kuma wasu sassan Tarayyar Turai.
- Sin: Ya Kamata A Gaggauta Farfado Da Tsarin Samar Da Na’urorin Semiconductor
- Gwamna Lawal Ya Lashe Kyautar Gwarzon Gwamnan Shekara Ta Jaridar LEADERSHIP
Babban Jami’in kula da lafiyar dabbobi na kasa, Dakta Samuel Anzaku ne ya fitar da wannan gargadi a cikin wasikar da aike wa da Daraktocin da ke kula da lafiyar dabbobi da ke jihohi 36 na kasar nan, ciki har da na Abuja.
Ya umarce jihohin da kuma masu kiwon kajin, da su tabbatar da sun fara gudanar da sanya ido kan dabbobin, domin dakile bazuwar cutar zuwa cikin jihohinsu.
Ya ce, an tabbatar da barkewar cutar a ranar 29 ga watan Dismabr 2025, da ta bulla a wani gidan gona da ke yankunan Newark-on-Trent da kuma Nottinghamshire.
“Idan ‘yan Nijeriya ba su manta ba, tuni dai gwamnatin kasar nan ta haramta shigo da kajin gidan gona zuwa cikin kasar nan da kuma namansu,“ in ji shi.
Ya kara da cewa, gwamnatin ta fito da wannan tsarin ne, domin karya kwarin guiwar shigo da kajin da kuma namansu zuwa cikin kasar, musamman domin a kara karfafa wa masu kiwon cikin gidan guiwa.















Discussion about this post