Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi watsi da zargin da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi cewa tsohon shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, na da hannu a sace Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
El-Rufai ya bayyana a wata hira da tashar Arise News cewa Ganduje ne matsalar Dadiyata, yana mai cewa gwamnatin Kaduna ba ta da alaƙa da lamarin. Ya kuma yi nuni da wani zargin furucin ɗan sanda da ya ce an turo daga Kano domin aiwatar da satar.
- Ɗan Ganduje Ya Gwangwaje Manoma, Da ‘Yan Kasuwa Da Manyan Kyautata A Kano
- Ka Manta Da Komai, Ka Bar Abba Ya Yi Wa Kano Aiki — Matar Ganduje Ga Kwankwaso
Sai dai Sanata Sani, ta shafinsa na X, ya ce Dadiyata fitaccen mai sukar gwamnatin Kaduna ne, ba gwamnatin Kano ko Ganduje ba. Ya ƙara da cewa an sace shi ne daga gidansa a unguwar Barnawa a ranar 1 ga Agusta, 2019, kuma har yanzu ba a san inda yake ba.
Ya kuma zargi cewa babu wata sanarwa ta hukuma daga gwamnatin Kaduna ko ziyara ga iyalansa tun bayan sacewar, yana mai cewa tsoro ya mamaye al’umma a lokacin. Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, ciki har da Amnesty International, sun taɓa kira da a gudanar da cikakken bincike kan lamarin, amma har yanzu ba a fitar da sakamakon hukuma ba.















Discussion about this post