Hukumar Kwallon Kafa ta Aljeriya (FAF) ta shigar da ƙara a hukumance ga Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) da kuma Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), kan hukuncin da alƙalin wasa ya yanke a wasan Kwata Fainal na gasar cin kofin nahiyar Afrika (AFCON 2025) tsakaninta da Nijeriya.
FAF ta sanar da wannan mataki ne a ranar Litinin ta shafinta na X, inda ta ce ƙarar ta biyo bayan abin da ta bayyana a matsayin alƙalanci mai cike da cece-kuce, tare da buƙatar a gudanar da cikakken bincike kan yadda aka tafiyar da wasan.
- Sin Da Aljeriya Na Fatan Bunkasa Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki
- Nijeriya Ce Ta Shida Wajen Sayar Da Man Fetur Kan Farashi Mai Sauki
A cewar hukumar, wasu muhimman hukunci da alƙalan wasan suka yanke sun janyo rashin gamsuwa a ɓangaren ƴan wasan Aljeriya da masu ruwa da tsaki, tana mai cewa alƙalanci ya saɓa ƙa’idojin aiki tare da jefa martabar alƙalancin ƙwallon ƙafa a Afrika cikin tambaya a idon duniya.

FAF ta ce ta gabatar da ƙorafin a hukumance domin a fayyace abin da ya faru tare da ɗaukar matakan da suka dace bisa ƙa’idojin CAF da FIFA. Wannan ƙarar ta biyo bayan rashin nasarar da Aljeriya ta sha a hannun Super Eagles ta Nijeriya da ci 2–0 a wasan da aka buga ranar Asabar, wanda ya fitar da ita daga gasar.















Discussion about this post