ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Damke Wani Mutum Kan Mutuwar Abokinsa A Wurin Liyafar Cin Abnici A Edo

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Rabiu Ali Indabawa

Rundunar ’Yansandan Jihar Edo ta tabbatar da kama wani mutum mai suna Eghosa Osas bisa zargin kashe abokinsa tun suna yara, Amadin Williams.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar, Eno Ikoedem, ta tabbatar da kamun ga PUNCH Metro.

Rundunar ta kara da cewa za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

ADVERTISEMENT

A cewar wata majiya da ke kusa da lamarin, marigayin ya dawo daga kasashen waje tare da iyalinsa domin bikin Kirsimeti.

An ce an kai masa hari tare da kashe shi ne a unguwar Oben, inda ya je halartar bikin liyafar bude sabon gida.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Majiyar ta ce, “Zan iya tabbatar da cewa Eghosa Osas mai shekaru 43 an kashe shi ne da hannun abokinsa tun suna yara, Amadin Williams, dalilan da suka jawo hakan kuma har yanzu ba a tabbatar da su ba.

“Marigayi Eghosa ya dawo daga kasashen waje ne domin yin bikin Kirsimeti tare da iyalinsa.

“An ce an kai masa hari tare da kashe shi a unguwar Oben, inda ya halarci bikin bude sabon gida.”

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Edo, Eno Ikoedem, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce babban dan’uwan marigayin ne ya kai rahoton kisan.

Ikoedem ta ce Eghosa ya fita ne domin yin bayan gida, sai wanda ake zargin ya tare shi ya sare shi da adda a wuya, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Ta kara da cewa wanda ake zargin ya tsere amma daga bisani aka kama shi a Birnin Benin, babban birnin Jihar Edo, inda ta jaddada cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ta ce, “Rahoton kisan Eghosa gaskiya ne, kuma wanda ake zargi, Amadin Williams, wanda ake kyautata zaton abokinsa ne tun suna yara, shi ne ake zargi da aikata laifin.”

“Bincike na ci gaba da gudana, kuma za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala shi (binciken),” in ji ta.

Wani makamancin lamari ya faru a watan Yuni, inda ’yansanda suka kama wani mutum mai shekaru 31, Joshua Osaigbobo, akan mutuwar budurwarsa, Osato Festus Edogiaweria mai shekaru 21, wadda aka ruwaito ta bace tun a watan Afrilun 2025.

’Yansanda sun ce sun fara bincike ne bayan mahaifiyar wacce aka kashe, Ojo, ta kai rahoton bacewar ’yarta a ofishin ’yan sanda na Aduwawa a ranar 25 ga Afrilun 2025.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Next Post
Manyan Nasarorin Da Dr Matawalle Ya Samar A Sashen Tsaro

Manyan Nasarorin Da Dr Matawalle Ya Samar A Sashen Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.