ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Damke Wani Mutum Kan Mutuwar Abokinsa A Wurin Liyafar Cin Abnici A Edo

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Rabiu Ali Indabawa

Rundunar ’Yansandan Jihar Edo ta tabbatar da kama wani mutum mai suna Eghosa Osas bisa zargin kashe abokinsa tun suna yara, Amadin Williams.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar, Eno Ikoedem, ta tabbatar da kamun ga PUNCH Metro.

Rundunar ta kara da cewa za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

ADVERTISEMENT

A cewar wata majiya da ke kusa da lamarin, marigayin ya dawo daga kasashen waje tare da iyalinsa domin bikin Kirsimeti.

An ce an kai masa hari tare da kashe shi ne a unguwar Oben, inda ya je halartar bikin liyafar bude sabon gida.

LABARAI MASU NASABA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Majiyar ta ce, “Zan iya tabbatar da cewa Eghosa Osas mai shekaru 43 an kashe shi ne da hannun abokinsa tun suna yara, Amadin Williams, dalilan da suka jawo hakan kuma har yanzu ba a tabbatar da su ba.

“Marigayi Eghosa ya dawo daga kasashen waje ne domin yin bikin Kirsimeti tare da iyalinsa.

“An ce an kai masa hari tare da kashe shi a unguwar Oben, inda ya halarci bikin bude sabon gida.”

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Edo, Eno Ikoedem, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce babban dan’uwan marigayin ne ya kai rahoton kisan.

Ikoedem ta ce Eghosa ya fita ne domin yin bayan gida, sai wanda ake zargin ya tare shi ya sare shi da adda a wuya, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Ta kara da cewa wanda ake zargin ya tsere amma daga bisani aka kama shi a Birnin Benin, babban birnin Jihar Edo, inda ta jaddada cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ta ce, “Rahoton kisan Eghosa gaskiya ne, kuma wanda ake zargi, Amadin Williams, wanda ake kyautata zaton abokinsa ne tun suna yara, shi ne ake zargi da aikata laifin.”

“Bincike na ci gaba da gudana, kuma za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala shi (binciken),” in ji ta.

Wani makamancin lamari ya faru a watan Yuni, inda ’yansanda suka kama wani mutum mai shekaru 31, Joshua Osaigbobo, akan mutuwar budurwarsa, Osato Festus Edogiaweria mai shekaru 21, wadda aka ruwaito ta bace tun a watan Afrilun 2025.

’Yansanda sun ce sun fara bincike ne bayan mahaifiyar wacce aka kashe, Ojo, ta kai rahoton bacewar ’yarta a ofishin ’yan sanda na Aduwawa a ranar 25 ga Afrilun 2025.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi
Tsaro

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
Next Post
Manyan Nasarorin Da Dr Matawalle Ya Samar A Sashen Tsaro

Manyan Nasarorin Da Dr Matawalle Ya Samar A Sashen Tsaro

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.