ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama ‘Yan Nijeriya Huɗu A Indiya Bisa Zargin Damfara Ta Intanet

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

An kama ƴan Nijeriya huɗu a ƙasar Indiya bisa zargin aikata damfara da satar shaidar mutane ta Intanet.

Jaridar PUNCH Metro ta rawaito daga rahotannin Times of India cewa an kama mutum uku da ake kira Chinedu, Sunday da Jules a hannun ƴansandan Gurugram saboda zargin damfarar mutane ta hanyar amfani da sunan mata a kafofin sada zumunta domin yaudarar waɗanda abin ya shafa.

An kama mutum na huɗu mai shekaru 49 da ake kira Uchenwa daga hannun rundunar musamman ta Uttar Pradesh a ranar Juma’a.

ADVERTISEMENT

Rahotanni sun ce ƴansanda sun ƙwato wayoyin hannu 19, kwamfuta guda ɗaya, da katunan SIM 18 na Indiya da na ƙasashen waje daga hannun Chinedu, Sunday da Jules.

Ƴansanda sun ce bincike ya fara ne bayan wani mutum ya kai ƙara a ranar 25 ga Afrilu na shekarar da ta gabata, yana cewa an damfare shi da wata mace da ya haɗu da ita a Instagram.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

“Wannan ƴar ta gaya masa cewa ta iso Indiya kuma tana buƙatar kuɗi Rs 69,900 a matsayin kuɗin rajista domin canja masa cek zuwa kuɗin Indiya a filin jirgin saman Mumbai,” in ji ƴansanda.

Bayan ya tura kuɗin, wanda aka damfarar ya gane cewa an yaudare shi.

A yayin bincike, ƴansanda sun bi sawun masu laifin har suka kama su a Noida da daddare a ranar Alhamis.

Rahotanni sun ce Sunday ya shiga Indiya ba bisa ƙa’ida ba ta Bangladesh a 2022, yayin da Chinedu da Jules suka shiga ƙasar da takardun karatu a 2018 da 2017.

“Waɗanda ake zargin suna tattaunawa da mutane a Indiya suna nuna kansu a matsayin mata a kafofin sada zumunta, suna amfani da amincewa da suka samu wajen damfara,” in ji wani jami’in ƴansanda.

A wani rahoto daban, an bayyana cewa Uchenwa yana ƙirƙirar bayanan bogi a kafofin sada zumunta, yana amfani da sunayen mutane daga Amurka da Birtaniya don yaudarar maza da mata a Indiya.

Rahotanni sun ce an riƙa yaudarar waɗanda abin ya shafa da alƙawarin aiko musu da kyaututtuka masu tsada, kuɗin waje da kayan alfarma zuwa Indiya.

Wani wanda abin ya shafa ya ce ya samu buƙatar abota a Facebook daga wata “Doris Williams” daga Ingila a watan Agusta 2025.

Bayan ya amince, an ce ta yi masa alƙawarin kawo kusan Rs 3 crore zuwa Indiya.

Daga baya aka ce wasu da ke nuna kansu a matsayin jami’an kwastam sun kira shi, suna cewa an tsare matar a filin jirgin saman Delhi saboda yawan kuɗin da take ɗauke da shi.

An tilasta masa biyan kuɗin “kwastam” har Rs 61,500 ta hanyar UPI.

Daga bisani kuma aka ci gaba da neman ƙarin kuɗi, har ya kai ga tura kusan Rs 40 lakh zuwa asusun daban-daban, sannan aka sake yaudararsa ya tura ƙarin Rs 28 lakh.

Binciken ya nuna cewa wanda ake zargi ya amsa cewa ya fara zuwa Indiya ne domin kasuwancin kayan sawa a shekarar 2010, amma daga baya ya koma harkar damfara ta intanet saboda matsalar kuɗi.

Waɗannan kama-kame na ƙara yawan rahotannin ƴan Nijeriya da ake dangantawa da laifuka a ƙasashen waje, ciki har da damfara, sata da safarar miyagun ƙwayoyi.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Sarki Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe kwana 25 A Hannun Masu Garkuwa A Kwara

'Yan Bindiga Sun Kashe Masu Ibada 3, Sun Sace 15 A Wani Coci A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

Majalisar Gudanarwa Ta Sin Ta Wallafa “Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Kan Kiyaye Lafiyar Al’ummar Kasar”

July 13, 2026
Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Xi Zai Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026, Inda Zai Gabatar Da Muhimmin Jawabi

July 13, 2026
Sin Ta Fitar Da Rahoton “Sake Karyata Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

Sin Ta Fitar Da Rahoton “Sake Karyata Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 13, 2026
Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.