ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Nijeriya

Kusan mako guda bayan rasuwar wata uwa ‘yar Nijeriya mai ‘ya’ya uku sakamakon cutar daji a kasar Burtaniya, an sake samun wani lamari mai ban tausayi inda wani uba dan Nijeriya mai ‘ya’ya uku, wanda aka bayyana sunansa da Herbert kawai, aka same shi a mace a cikin gidansa.

Marigayin ya bar mata da ‘ya’ya uku kanana, yayin da iyalansa ke neman tallafin kudi domin gudanar da jana’izarsa da kuma mayar da gawarsa gida Nijeriya.

Rahotanni sun nuna cewa Herbert, wanda ke zaune a Thornaby, ya mutu ne a cikin barci a makon da ya gabata, lamarin da iyalansa suka bayyana a matsayin abin girgiza da radadi.

ADVERTISEMENT

Wani mai amfani da dandalin D mai suna “The Stress Manager” ya bayyana cewa marigayin yana fuskantar matsananciyar damuwa ta zuciya da ta kudi bayan rasuwar mahaifinsa a Nijeriya kwanaki kadan kafin mutuwarsa.

Ya ce: “Herbert mutum ne mai nutsuwa kuma uba mai kula da iyalinsa. Ya rasu kwatsam a cikin barci a Thornaby.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

“Kwanaki kadan kafin rasuwarsa, yana cikin jimamin rasuwar mahaifinsa a Nijeriya. Bai samu damar zuwa jana’izar ba, amma ya kashe duk abin da yake da shi domin ganin an yi masa jana’iza mai kyau. Wannan ya jefa shi cikin matsananciyar damuwa da rashin kudi.

“Sai ga abin da ba a zata ba ya faru—Herbert ya rasu a ranar da aka binne mahaifinsa.”

An kuma bayyana cewa abin ya fi muni saboda ‘ya’yansa ne suka fara gano gawarsa da safe, yayin da matarsa ba ta gida a lokacin.

A halin yanzu, matarsa na fuskantar nauyin kula da ‘ya’yansu uku tare da wahalar kudin jana’iza da mayar da gawar gida.

Tsohon shugaban ‘yan Nijeriya a Birtaniya, Benjamin Kuti, ya tabbatar da rasuwar Herbert tare da kira ga al’ummar ‘yan Nijeriya da su taimaka wa iyalansa.

An kuma kaddamar da wani shirin tara kudi domin tallafa wa iyalan, inda zuwa lokacin rubuta rahoton an tara fam £2,633 daga cikin burin £7,000.

A baya dai, an ruwaito rasuwar wata uwa ‘yar Nijeriya mai ‘ya’ya uku, Omotayo Abioye, wadda ta mutu sakamakon cutar sankarar mama tana da shekaru 40, lamarin da ya kara jefa al’umma cikin jimami.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Farfesa Abdalla Uba Adamu Ya Yi Ritaya Bayan Shekaru 46 Na Aiki

Farfesa Abdalla Uba Adamu Ya Yi Ritaya Bayan Shekaru 46 Na Aiki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.