ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Allah-wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Kasuwar Hausawa A Edo

by Sani Anwar
8 months ago
Allah

Gamayyar Ƙungiyoyin Arewa (CNG), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wa ƴan kasuwar Hausawa a Ekpoma da ke gundumar Edo ta tsakiya, inda ta bayyana lamarin a matsayin wani abin da bai dace ba da zai iya ta’azzara rikicin ƙabilanci, idan ba a gaggauta magance su ba.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin ta hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi, ta bayyana rashin jin daɗinta kan rahotannin da ke cewa; wasu matasa sun fatattaki ƴan kasuwar Hausawa daga kasuwar dabbobi tare da yanka akuyoyinsu, biyo bayan kashe wani matashin yankin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka yi.

  • Zargin Barin Almakashin Tiyata Acikin Wata Mata Ya Yi Ajalin Mutuwarta A Kano
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Watsi Da Aniyar Amfani Da Karfi Kan Iran

A cewar CNG, an ga ƴan kasuwar Hausa na tserewa daga kasuwar cikin fargaba, suna barin dabbobinsu, yayin da wasu mazauna yankin suka ci gaba da yin ɓarna ta hanyar kashe dabbobin da aka bari.

ADVERTISEMENT

Yayin da ta ke nuna baƙin ciki da ɓacin rai da ke tattare da kisan gillar da aka yi wa matasan yankin, ƙungiyar ta jaddada cewa; ba za a amince da kai wa ƴan kasuwar da ba su ji ba, ba su gani ba, wanda hakan ya zama wani babban rashin adalci.

Charanchi ya ƙara da cewa, “Ayyukan da wasu mutane da suka ɗauki doka a hannunsu, ba na dabbanci ba ne kawai, illa dai na lalata tsarin al’ummarmu ne.” “An tilasta wa ƴan kasuwarmu tserewa, don tsira da rayukansu, sun bar dukiyoyinsu, an ci gaba da yi musu ɓarna.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Gamayyar ƙungiyoyin, ta yi gargaɗin cewa; barin irin wannan lamari ba tare da la’akari da shi ba, zai iya haifar da tashin hankali tsakanin al’umma da kuma lalata dangantakar da ke tsakanin al’ummomin da suka yi zaman lafiya a tsawon lokaci.

Ƙungiyar ta CNG, ta yi kira ga gwamnatin Jihar Edo, da ta ɗauki matakin gaggawa; don kare rayuka da dukiyoyin ɗaukacin mazauna yankin, ba tare da la’akari da ƙabila ko yare ba. Ƙungiyar ta ce, za ta ɗora wa gwamnatin jihar alhakin tabbatar da tsaron al’ummar Hausawa a Edo ta tsakiya da sauran sassan jihar.

“Al’ummar Hausawa, kamar kowace ƙabila a Nijeriya, sun cancanci zama lafiya da tsaro,” in ji Charanchi. “Ba za mu ƙara sanya ido ana kai wa mutanenmu hari da kuma ware su a wuraren da suke zama a matsayin ƴan tsiraru ba.”

Allah
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.