ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Allah-wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Kasuwar Hausawa A Edo

by Sani Anwar
6 months ago
Allah

Gamayyar Ƙungiyoyin Arewa (CNG), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wa ƴan kasuwar Hausawa a Ekpoma da ke gundumar Edo ta tsakiya, inda ta bayyana lamarin a matsayin wani abin da bai dace ba da zai iya ta’azzara rikicin ƙabilanci, idan ba a gaggauta magance su ba.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin ta hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi, ta bayyana rashin jin daɗinta kan rahotannin da ke cewa; wasu matasa sun fatattaki ƴan kasuwar Hausawa daga kasuwar dabbobi tare da yanka akuyoyinsu, biyo bayan kashe wani matashin yankin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka yi.

  • Zargin Barin Almakashin Tiyata Acikin Wata Mata Ya Yi Ajalin Mutuwarta A Kano
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Watsi Da Aniyar Amfani Da Karfi Kan Iran

A cewar CNG, an ga ƴan kasuwar Hausa na tserewa daga kasuwar cikin fargaba, suna barin dabbobinsu, yayin da wasu mazauna yankin suka ci gaba da yin ɓarna ta hanyar kashe dabbobin da aka bari.

ADVERTISEMENT

Yayin da ta ke nuna baƙin ciki da ɓacin rai da ke tattare da kisan gillar da aka yi wa matasan yankin, ƙungiyar ta jaddada cewa; ba za a amince da kai wa ƴan kasuwar da ba su ji ba, ba su gani ba, wanda hakan ya zama wani babban rashin adalci.

Charanchi ya ƙara da cewa, “Ayyukan da wasu mutane da suka ɗauki doka a hannunsu, ba na dabbanci ba ne kawai, illa dai na lalata tsarin al’ummarmu ne.” “An tilasta wa ƴan kasuwarmu tserewa, don tsira da rayukansu, sun bar dukiyoyinsu, an ci gaba da yi musu ɓarna.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

Gamayyar ƙungiyoyin, ta yi gargaɗin cewa; barin irin wannan lamari ba tare da la’akari da shi ba, zai iya haifar da tashin hankali tsakanin al’umma da kuma lalata dangantakar da ke tsakanin al’ummomin da suka yi zaman lafiya a tsawon lokaci.

Ƙungiyar ta CNG, ta yi kira ga gwamnatin Jihar Edo, da ta ɗauki matakin gaggawa; don kare rayuka da dukiyoyin ɗaukacin mazauna yankin, ba tare da la’akari da ƙabila ko yare ba. Ƙungiyar ta ce, za ta ɗora wa gwamnatin jihar alhakin tabbatar da tsaron al’ummar Hausawa a Edo ta tsakiya da sauran sassan jihar.

“Al’ummar Hausawa, kamar kowace ƙabila a Nijeriya, sun cancanci zama lafiya da tsaro,” in ji Charanchi. “Ba za mu ƙara sanya ido ana kai wa mutanenmu hari da kuma ware su a wuraren da suke zama a matsayin ƴan tsiraru ba.”

Allah
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.