ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Allah-wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Kasuwar Hausawa A Edo

by Sani Anwar
5 months ago
Allah

Gamayyar Ƙungiyoyin Arewa (CNG), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wa ƴan kasuwar Hausawa a Ekpoma da ke gundumar Edo ta tsakiya, inda ta bayyana lamarin a matsayin wani abin da bai dace ba da zai iya ta’azzara rikicin ƙabilanci, idan ba a gaggauta magance su ba.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Litinin ta hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi, ta bayyana rashin jin daɗinta kan rahotannin da ke cewa; wasu matasa sun fatattaki ƴan kasuwar Hausawa daga kasuwar dabbobi tare da yanka akuyoyinsu, biyo bayan kashe wani matashin yankin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka yi.

  • Zargin Barin Almakashin Tiyata Acikin Wata Mata Ya Yi Ajalin Mutuwarta A Kano
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Watsi Da Aniyar Amfani Da Karfi Kan Iran

A cewar CNG, an ga ƴan kasuwar Hausa na tserewa daga kasuwar cikin fargaba, suna barin dabbobinsu, yayin da wasu mazauna yankin suka ci gaba da yin ɓarna ta hanyar kashe dabbobin da aka bari.

ADVERTISEMENT

Yayin da ta ke nuna baƙin ciki da ɓacin rai da ke tattare da kisan gillar da aka yi wa matasan yankin, ƙungiyar ta jaddada cewa; ba za a amince da kai wa ƴan kasuwar da ba su ji ba, ba su gani ba, wanda hakan ya zama wani babban rashin adalci.

Charanchi ya ƙara da cewa, “Ayyukan da wasu mutane da suka ɗauki doka a hannunsu, ba na dabbanci ba ne kawai, illa dai na lalata tsarin al’ummarmu ne.” “An tilasta wa ƴan kasuwarmu tserewa, don tsira da rayukansu, sun bar dukiyoyinsu, an ci gaba da yi musu ɓarna.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gamayyar ƙungiyoyin, ta yi gargaɗin cewa; barin irin wannan lamari ba tare da la’akari da shi ba, zai iya haifar da tashin hankali tsakanin al’umma da kuma lalata dangantakar da ke tsakanin al’ummomin da suka yi zaman lafiya a tsawon lokaci.

Ƙungiyar ta CNG, ta yi kira ga gwamnatin Jihar Edo, da ta ɗauki matakin gaggawa; don kare rayuka da dukiyoyin ɗaukacin mazauna yankin, ba tare da la’akari da ƙabila ko yare ba. Ƙungiyar ta ce, za ta ɗora wa gwamnatin jihar alhakin tabbatar da tsaron al’ummar Hausawa a Edo ta tsakiya da sauran sassan jihar.

“Al’ummar Hausawa, kamar kowace ƙabila a Nijeriya, sun cancanci zama lafiya da tsaro,” in ji Charanchi. “Ba za mu ƙara sanya ido ana kai wa mutanenmu hari da kuma ware su a wuraren da suke zama a matsayin ƴan tsiraru ba.”

Allah
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Daƙile Hare-Haren Ƴan Ta’adda, Sun Kwato Makamai A Borno Da Adamawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.