ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Saita Wa Gwamna Yusuf Hanyar Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Sani Anwar
8 months ago
Tinubu

Biyo bayan wata ganawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano suka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, alamu sun nuna cewa; gwamnan na shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Wasu majiyoyi da ke da masaniya kan taron, sun shaida wa manema labarai cewa; tattaunawar ta warware matsalolin siyasa da tun farko suka kawo cikas ga yunƙurin sauya sheƙar da gwamnan ke shirin yi.

Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da ake ta cece-kuce a kan siyasar Kano, makwannin da suka gabata, inda rahotanni suka bayyana aniyar ta Yusuf na shiga jam’iyyar APC a matsayin wadda ta mamaye tarukan jama’a tare da dagula dangantakarsa da tsohon gwamna, kuma jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda majiyoyi suka bayyana, ƙoƙarin da Yusuf ya yi a ƴan makwannin nan, na da nasaba da rashin tabbas kan makomarsa ta siyasa a cikin jam’iyyar APC, musamman tabbacin da ya bayar game da sake tsayawa takara a 2027, da makomar tsarin siyasarsa a halin yanzu da kuma tsaron lafiyar magoya bayansa a cikin jam’iyyar mai mulki.

  • Sin Ta Mika Sakon Ta’azziya Sakamakon Gobara Da Ta Kone Wani Babban Kanti A Pakistan
  • Jita-jitar Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Na Ganawar Sirri Da Tinubu A Aso Rock

Waɗancan batutuwa, in ji masu lura da al’amuran, an magance su ne a ganawar da suka yi da shugaba Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Har ila yau, gwamna Yusuf ya ƙi yarda ya yi magana da manema labarai, bayan barinsa Villa, inda ya bayyana cewa, “zai sake dawowa.”

Rahotannin sun ce, an kwashe kusan sa’o’i uku ana ganawar. Domin kuwa, gwamnan ya isa fadar shugaban ƙasa ne tun misalin ƙarfe 4:10 na yamma, sanye da farar babban riga da jar hula, sannan ya bar fadar da bayan ƙarfe 7 na dare.

Tun a ƙarshen shekarar da ta gabata ne, ake ta faman cece-kuce kan batun sauya sheƙar ta Yusuf, biyo bayan dambarwar siyasar da ke nuni da sake daidaita alaƙarsa da gwamnatin tarayya, ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Duk da cewa, gwamnan ya yi shiru a bainar jama’a a kan lamarin, amma wasu daga cikin muƙarrabansa da abokan siyasa a ƴan watannin nan, sun fito fili sun tattauna da shugabannin jam’iyyar APC a Kano da Abuja, lamarin da ya ƙara rura wutar tsammanin ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai, rahotanni a makon da ya gabata sun nuna cewa; shirin sauya sheƙar ya gamu da cikas bayan da aka ce shugabannin jam’iyyar APC, sun yi taka-tsan-tsan wajen bayar da ƙwaƙaran alƙawura, musamman kan batun tikitin sake komawa takarar gwamna kai tsaye a shekarar 2027.

Rahotanni sun nuna cewa, wannan jinkirin ya tilasta wa gwamnan yin tafiyar hawainiya, duk da cewa; wasu magoya bayansa a matakin ƙananan hukumomi da na unguwanni sun yi taro tare da nuna goyon bayan sauya sheƙar.

Ga dukkan alamu, ganawar ta ranar Litinin da shugaba Tinubu, ta sake farfaɗo da batun sayin sheƙar.

Majiyoyi sun ce, shugaban da kansa ya tabbatar wa Yusuf ƙimarsa ga lissafin siyasar APC, musamman a Kano da yankin Arewa maso Yamma, inda jam’iyyar ta sha kaye a zaben 2023.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Tinubu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.