ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Saita Wa Gwamna Yusuf Hanyar Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Sani Anwar
5 months ago
Tinubu

Biyo bayan wata ganawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano suka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, alamu sun nuna cewa; gwamnan na shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Wasu majiyoyi da ke da masaniya kan taron, sun shaida wa manema labarai cewa; tattaunawar ta warware matsalolin siyasa da tun farko suka kawo cikas ga yunƙurin sauya sheƙar da gwamnan ke shirin yi.

Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da ake ta cece-kuce a kan siyasar Kano, makwannin da suka gabata, inda rahotanni suka bayyana aniyar ta Yusuf na shiga jam’iyyar APC a matsayin wadda ta mamaye tarukan jama’a tare da dagula dangantakarsa da tsohon gwamna, kuma jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda majiyoyi suka bayyana, ƙoƙarin da Yusuf ya yi a ƴan makwannin nan, na da nasaba da rashin tabbas kan makomarsa ta siyasa a cikin jam’iyyar APC, musamman tabbacin da ya bayar game da sake tsayawa takara a 2027, da makomar tsarin siyasarsa a halin yanzu da kuma tsaron lafiyar magoya bayansa a cikin jam’iyyar mai mulki.

  • Sin Ta Mika Sakon Ta’azziya Sakamakon Gobara Da Ta Kone Wani Babban Kanti A Pakistan
  • Jita-jitar Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Na Ganawar Sirri Da Tinubu A Aso Rock

Waɗancan batutuwa, in ji masu lura da al’amuran, an magance su ne a ganawar da suka yi da shugaba Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Har ila yau, gwamna Yusuf ya ƙi yarda ya yi magana da manema labarai, bayan barinsa Villa, inda ya bayyana cewa, “zai sake dawowa.”

Rahotannin sun ce, an kwashe kusan sa’o’i uku ana ganawar. Domin kuwa, gwamnan ya isa fadar shugaban ƙasa ne tun misalin ƙarfe 4:10 na yamma, sanye da farar babban riga da jar hula, sannan ya bar fadar da bayan ƙarfe 7 na dare.

Tun a ƙarshen shekarar da ta gabata ne, ake ta faman cece-kuce kan batun sauya sheƙar ta Yusuf, biyo bayan dambarwar siyasar da ke nuni da sake daidaita alaƙarsa da gwamnatin tarayya, ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Duk da cewa, gwamnan ya yi shiru a bainar jama’a a kan lamarin, amma wasu daga cikin muƙarrabansa da abokan siyasa a ƴan watannin nan, sun fito fili sun tattauna da shugabannin jam’iyyar APC a Kano da Abuja, lamarin da ya ƙara rura wutar tsammanin ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai, rahotanni a makon da ya gabata sun nuna cewa; shirin sauya sheƙar ya gamu da cikas bayan da aka ce shugabannin jam’iyyar APC, sun yi taka-tsan-tsan wajen bayar da ƙwaƙaran alƙawura, musamman kan batun tikitin sake komawa takarar gwamna kai tsaye a shekarar 2027.

Rahotanni sun nuna cewa, wannan jinkirin ya tilasta wa gwamnan yin tafiyar hawainiya, duk da cewa; wasu magoya bayansa a matakin ƙananan hukumomi da na unguwanni sun yi taro tare da nuna goyon bayan sauya sheƙar.

Ga dukkan alamu, ganawar ta ranar Litinin da shugaba Tinubu, ta sake farfaɗo da batun sayin sheƙar.

Majiyoyi sun ce, shugaban da kansa ya tabbatar wa Yusuf ƙimarsa ga lissafin siyasar APC, musamman a Kano da yankin Arewa maso Yamma, inda jam’iyyar ta sha kaye a zaben 2023.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.