ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Saita Wa Gwamna Yusuf Hanyar Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Sani Anwar
6 months ago
Tinubu

Biyo bayan wata ganawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano suka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, alamu sun nuna cewa; gwamnan na shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Wasu majiyoyi da ke da masaniya kan taron, sun shaida wa manema labarai cewa; tattaunawar ta warware matsalolin siyasa da tun farko suka kawo cikas ga yunƙurin sauya sheƙar da gwamnan ke shirin yi.

Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da ake ta cece-kuce a kan siyasar Kano, makwannin da suka gabata, inda rahotanni suka bayyana aniyar ta Yusuf na shiga jam’iyyar APC a matsayin wadda ta mamaye tarukan jama’a tare da dagula dangantakarsa da tsohon gwamna, kuma jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda majiyoyi suka bayyana, ƙoƙarin da Yusuf ya yi a ƴan makwannin nan, na da nasaba da rashin tabbas kan makomarsa ta siyasa a cikin jam’iyyar APC, musamman tabbacin da ya bayar game da sake tsayawa takara a 2027, da makomar tsarin siyasarsa a halin yanzu da kuma tsaron lafiyar magoya bayansa a cikin jam’iyyar mai mulki.

  • Sin Ta Mika Sakon Ta’azziya Sakamakon Gobara Da Ta Kone Wani Babban Kanti A Pakistan
  • Jita-jitar Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Na Ganawar Sirri Da Tinubu A Aso Rock

Waɗancan batutuwa, in ji masu lura da al’amuran, an magance su ne a ganawar da suka yi da shugaba Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Har ila yau, gwamna Yusuf ya ƙi yarda ya yi magana da manema labarai, bayan barinsa Villa, inda ya bayyana cewa, “zai sake dawowa.”

Rahotannin sun ce, an kwashe kusan sa’o’i uku ana ganawar. Domin kuwa, gwamnan ya isa fadar shugaban ƙasa ne tun misalin ƙarfe 4:10 na yamma, sanye da farar babban riga da jar hula, sannan ya bar fadar da bayan ƙarfe 7 na dare.

Tun a ƙarshen shekarar da ta gabata ne, ake ta faman cece-kuce kan batun sauya sheƙar ta Yusuf, biyo bayan dambarwar siyasar da ke nuni da sake daidaita alaƙarsa da gwamnatin tarayya, ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Duk da cewa, gwamnan ya yi shiru a bainar jama’a a kan lamarin, amma wasu daga cikin muƙarrabansa da abokan siyasa a ƴan watannin nan, sun fito fili sun tattauna da shugabannin jam’iyyar APC a Kano da Abuja, lamarin da ya ƙara rura wutar tsammanin ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai, rahotanni a makon da ya gabata sun nuna cewa; shirin sauya sheƙar ya gamu da cikas bayan da aka ce shugabannin jam’iyyar APC, sun yi taka-tsan-tsan wajen bayar da ƙwaƙaran alƙawura, musamman kan batun tikitin sake komawa takarar gwamna kai tsaye a shekarar 2027.

Rahotanni sun nuna cewa, wannan jinkirin ya tilasta wa gwamnan yin tafiyar hawainiya, duk da cewa; wasu magoya bayansa a matakin ƙananan hukumomi da na unguwanni sun yi taro tare da nuna goyon bayan sauya sheƙar.

Ga dukkan alamu, ganawar ta ranar Litinin da shugaba Tinubu, ta sake farfaɗo da batun sayin sheƙar.

Majiyoyi sun ce, shugaban da kansa ya tabbatar wa Yusuf ƙimarsa ga lissafin siyasar APC, musamman a Kano da yankin Arewa maso Yamma, inda jam’iyyar ta sha kaye a zaben 2023.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Next Post
Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.