ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Saita Wa Gwamna Yusuf Hanyar Sauya Sheƙa Zuwa APC

by Sani Anwar
4 months ago
Tinubu

Biyo bayan wata ganawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano suka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin, alamu sun nuna cewa; gwamnan na shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Wasu majiyoyi da ke da masaniya kan taron, sun shaida wa manema labarai cewa; tattaunawar ta warware matsalolin siyasa da tun farko suka kawo cikas ga yunƙurin sauya sheƙar da gwamnan ke shirin yi.

Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da ake ta cece-kuce a kan siyasar Kano, makwannin da suka gabata, inda rahotanni suka bayyana aniyar ta Yusuf na shiga jam’iyyar APC a matsayin wadda ta mamaye tarukan jama’a tare da dagula dangantakarsa da tsohon gwamna, kuma jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda majiyoyi suka bayyana, ƙoƙarin da Yusuf ya yi a ƴan makwannin nan, na da nasaba da rashin tabbas kan makomarsa ta siyasa a cikin jam’iyyar APC, musamman tabbacin da ya bayar game da sake tsayawa takara a 2027, da makomar tsarin siyasarsa a halin yanzu da kuma tsaron lafiyar magoya bayansa a cikin jam’iyyar mai mulki.

  • Sin Ta Mika Sakon Ta’azziya Sakamakon Gobara Da Ta Kone Wani Babban Kanti A Pakistan
  • Jita-jitar Sauya Sheƙa: Gwamna Yusuf Na Ganawar Sirri Da Tinubu A Aso Rock

Waɗancan batutuwa, in ji masu lura da al’amuran, an magance su ne a ganawar da suka yi da shugaba Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Har ila yau, gwamna Yusuf ya ƙi yarda ya yi magana da manema labarai, bayan barinsa Villa, inda ya bayyana cewa, “zai sake dawowa.”

Rahotannin sun ce, an kwashe kusan sa’o’i uku ana ganawar. Domin kuwa, gwamnan ya isa fadar shugaban ƙasa ne tun misalin ƙarfe 4:10 na yamma, sanye da farar babban riga da jar hula, sannan ya bar fadar da bayan ƙarfe 7 na dare.

Tun a ƙarshen shekarar da ta gabata ne, ake ta faman cece-kuce kan batun sauya sheƙar ta Yusuf, biyo bayan dambarwar siyasar da ke nuni da sake daidaita alaƙarsa da gwamnatin tarayya, ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Duk da cewa, gwamnan ya yi shiru a bainar jama’a a kan lamarin, amma wasu daga cikin muƙarrabansa da abokan siyasa a ƴan watannin nan, sun fito fili sun tattauna da shugabannin jam’iyyar APC a Kano da Abuja, lamarin da ya ƙara rura wutar tsammanin ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai, rahotanni a makon da ya gabata sun nuna cewa; shirin sauya sheƙar ya gamu da cikas bayan da aka ce shugabannin jam’iyyar APC, sun yi taka-tsan-tsan wajen bayar da ƙwaƙaran alƙawura, musamman kan batun tikitin sake komawa takarar gwamna kai tsaye a shekarar 2027.

Rahotanni sun nuna cewa, wannan jinkirin ya tilasta wa gwamnan yin tafiyar hawainiya, duk da cewa; wasu magoya bayansa a matakin ƙananan hukumomi da na unguwanni sun yi taro tare da nuna goyon bayan sauya sheƙar.

Ga dukkan alamu, ganawar ta ranar Litinin da shugaba Tinubu, ta sake farfaɗo da batun sayin sheƙar.

Majiyoyi sun ce, shugaban da kansa ya tabbatar wa Yusuf ƙimarsa ga lissafin siyasar APC, musamman a Kano da yankin Arewa maso Yamma, inda jam’iyyar ta sha kaye a zaben 2023.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.