Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa reshen jami’ar Jos ta yi gargaɗin cewa jami’o’in gwamnati a Nijeriya na iya sake tsunduma wani sabon yajin aiki sakamakon abin da ta bayyana a matsayin gaza cika yarjejeniyar 2025 da aka ƙulla tsakanin gwamnatin tarayya da ASUU.
Shugaban reshen ƙungiyar, Joseph Molwus, ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai ranar Litinin, inda ya ce majalisar zartarwar ASUU ta ƙasa ta nuna damuwa kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar da aka rattabawa hannu ranar 23 ga Disamba, 2025.
Ƙungiyar ta ce har yanzu akwai batutuwan da suka haɗa da rashin biyan albashin watanni uku da rabi da aka riƙe bayan yajin aikin 2022, bashin ƙarin girma, da matsalolin albashi da suka shafi tsarin biyan albashi na bai ɗaya, da kuma wasu haƙƙoƙin malamai da ba a biya ba.
ASUU ta kuma soki wasu manufofin ilimi na baya-bayan nan da gwamnatin tarayya ke ƙoƙarin aiwatarwa, ciki har da janye tsarin koyar da harshen uwa da kuma shirin kafa reshen Coventry University a Nijeriya.
Sai dai ƙungiyar ta yabawa Sa’adu Zungur University da jami’ar Ekiti bisa aiwatar da ɓangaren albashi na yarjejeniyar, tana mai kira ga sauran jami’o’i da gwamnatoci da su bi sahu domin kaucewa sake rufe jami’o’in gwamnati a faɗin ƙasar nan.















Discussion about this post