Tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Sanata Datti Baba-Ahmed, ya ce tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya fara neman manyan muƙaman siyasa tun lokacin da shi Baba-Ahmed ke yi wa ƙasa hidima (NYSC). Ya ce hakan na nuna cewa Nijeriya na matuƙar buƙatar sabon ƙarni na shugabanni masu sabbin tunani da dabaru.
Baba-Ahmed ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da tashar Channels Television a ranar Juma’a, inda ya yi tambaya kan dalilin da ya sa tsofaffin ’yan siyasa ke ci gaba da mamaye fagen mukamai a ƙasar. Ya ce sun yi takara tare da Atiku a zaɓukan fidda gwani na 2018, sannan kuma a 2023 sun sake fafatawa, yana mai cewa sake fitowar irin waɗannan mutane a 2027 na ƙara jaddada buƙatar sauyin shugabanci.
- Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed
- 2027: Datti Baba-Ahmed Ya Ayana Neman Takarar Shugaban Ƙasa
A cewarsa, Najeriya ba ta rasa ƙwararru da masu basira da za su iya warware matsalolin ƙasar ba, sai dai tsarin siyasar ƙasar ne ke hana su shiga. Ya bayyana tsarin a matsayin mai tsada, mai wahala, kuma cike da masu riƙe da madafun iko da kuma alkawuran da ba a cikawa.
Baba-Ahmed ya ƙara da cewa tsadar kamfen, da tasirin masu hannu da shuni a siyasa, da tsarin siyasar uban gida na ci gaba da toshe damar matasa da masu neman sauyi daga shiga siyasa yadda ya kamata. Ya ce akwai wani sabon ƙarni na ’yan Nijeriya da ke jiran sabon jagora, mai yiyuwa ma daga wata sabuwar jam’iyya, wadda zai ja ragamar canji a ƙasar nan yayin da shirye-shiryen siyasa gabanin zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar zafi.















Discussion about this post