Xi Ya Taya Carlos Vila Nova Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Sao Tome Da Principe
A yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya taya Carlos Vila Nova murnar sake lashe zaben shugaban kasar...
A yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya taya Carlos Vila Nova murnar sake lashe zaben shugaban kasar...
A yau Laraba, hukumar kula da hakkokin mallakar sabbin kirkire-kirkire ta kasar Sin (CNIPA) ta bayyana cewa, ya zuwa karshen...
A kwanan nan, hukumar bunkasa ilimi da kimiyya da fasaha da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya, watau UNESCO ta kara...
Yanzu dai, karin sabbin abubuwa iri uku kirar Sin masu lakabin “New ‘New Three’’’ wadanda suka kunshi mutum-mutumin inji, da...
Firaministan kasar Sin, Li Qiang, ya jaddada bukatar ci gaba da karfafa kwazon kasar Sin wajen rigakafin abkuwar ibtla’i, da...
Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya halarci wani taro na manyan jami’ai da aka shirya bisa cika shekaru...
A yau Talata ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya bayyana cewa bai kamata manufar alakar kasa da kasa, da hadin gwiwar sassa daban daban ta zama kaiwa wani bangare na daban hari ba. Lin, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, lokacin da aka bukaci ya yi tsokaci game da wasu rahotanni, masu cewa Amurka na shirin kara daruruwan miliyoyin dala da take kashewa, da nufin dakile karuwar tasirin da Sin ke samu a sassan nahiyar Amurka, da Afirka da Asiya. Jami’in, ya ce kasar Sin na adawa da kafa duk wani rukuni na mayar da wasu sassa saniyar-ware, kuma duk wani hadin gwiwa da Sin ke yi da wasu sassan kasashe da yankuna, musamman ma da kasashe masu tasowa, ba tana yinsa ba ne da nufin kafa rukuni, ko yin adawa da wani bangare, maimakon haka tana hada karfi da karfe ne da sauran sassan duniya da nufin kare zaman lafiyar duniya, da ingiza ci gaban duniya, da daga matsayin odar kasa da kasa, da gina al’ummar duniya mai makomar bai daya. Lin Jian, ya kuma yi tir da siyasantar da batun shimfida wayoyin sadarwa na karkashin teku, yana mai cewa yin hakan zai gurgunta tsarin gudanar da kasuwanni na kasa da kasa. Kalaman nasa sun biyo bayan wasu rahotanni dake cewa Amurka, ta bayyana damuwa game da shigar kasar Sin cikin aikin shimfida wayoyin sadarwa a sassan tekun Fasifik. (Saminu Alhassan)
Ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ta fitar da takarda mai taken “Matsayin Sin kan abin da ake kira da ‘samar...
Mataimakin shugaban sashen cinikin waje na ma’aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin He Shaojun, ya bayyana a gun taron manema...
Kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fidda muhimmin bayani kan ayyuka masu nasaba da Sinawan dake kasashen ketare....
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.