ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
kwankwasiyya

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi Allah-wadai da kiran da aka yi na a sauke Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, tana mai bayyana shi a matsayin abu mai tayar da hankali, da rashin godiya da kuma abin da ba bazu su yarda da shi ba.

Wannan matsaya na ƙungiyar na cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Dr. Habibu Saleh Mailemo, ya fitar a ranar Alhamis, biyo bayan rahotannin da ke yawo kan cewa gwamnatin jihar ta buƙaci mataimakin gwamnan ya yi murabus ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida.

  • NNPP Ta Caccaki Gwamna Yusuf Kan Ficewa Daga Jam’iyyar, Ta Ce “Cin Amanar Kano Da Kwankwasiyya Ne”
  • Siyasar Kano: Kwankwaso Ya Bayyana 23 Ga Janairu A Matsayin Ranar Cin Amana

Kwankwasiyya ta ce ta karɓi rahoton “da matuƙar damuwa,” tana mai cewa irin wannan kira ba shi da hujja kuma na iya barazana ga zaman lafiya da jituwa ta dimokuraɗiyya a jihar. “Wannan kira ba shi da tushe, yana iya tayar da hankali, kuma abin takaici ne ƙwarai. Yana ƙarfafa zargin da ke ƙara yaduwa a zuƙatan al’ummar Kano cewa gwamnatin yanzu ba ta da niyyar tabbatar da ɗorewar  zaman lafiyar siyasa jihar, daidaito na cikin gida da jure ra’ayoyi,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta zargi gwamnatin da yunƙurin warewa da wulaƙanta magoya bayan Jagoranta na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda ta ce ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar gwamnatin mai ci. Ta jaddada cewa an zaɓi mataimakin gwamnan ne tare da gwamna a kan tikitin haɗin gwuiwa, don haka ba za a iya tilasta masa barin ofis bisa son rai na wasu mutane a cikin gwamnati ba.

Kwankwasiyya ta kuma ce idan gwamnatin na da wata fahimta ta adalcin siyasa, ya dace ta waiwayi abubuwan da suka faru a zaɓukan 2019 da 2023, inda Jagora Kwankwaso da miliyoyin magoya bayansa suka yi gagarumar sadaukarwa wajen samun nasarar da ta kai Gwamna Abba Kabir Yusuf da Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo zuwa Gidan Gwamnati. Ta ƙara da cewa ba za ta yi shiru ba a kan abin da ta kira cin amanar magoya baya, da tsoratarwa da wulakanta mambobinta masu biyayya.

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

kwankwasiyya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.