ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
kwankwasiyya

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi Allah-wadai da kiran da aka yi na a sauke Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, tana mai bayyana shi a matsayin abu mai tayar da hankali, da rashin godiya da kuma abin da ba bazu su yarda da shi ba.

Wannan matsaya na ƙungiyar na cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Dr. Habibu Saleh Mailemo, ya fitar a ranar Alhamis, biyo bayan rahotannin da ke yawo kan cewa gwamnatin jihar ta buƙaci mataimakin gwamnan ya yi murabus ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida.

  • NNPP Ta Caccaki Gwamna Yusuf Kan Ficewa Daga Jam’iyyar, Ta Ce “Cin Amanar Kano Da Kwankwasiyya Ne”
  • Siyasar Kano: Kwankwaso Ya Bayyana 23 Ga Janairu A Matsayin Ranar Cin Amana

Kwankwasiyya ta ce ta karɓi rahoton “da matuƙar damuwa,” tana mai cewa irin wannan kira ba shi da hujja kuma na iya barazana ga zaman lafiya da jituwa ta dimokuraɗiyya a jihar. “Wannan kira ba shi da tushe, yana iya tayar da hankali, kuma abin takaici ne ƙwarai. Yana ƙarfafa zargin da ke ƙara yaduwa a zuƙatan al’ummar Kano cewa gwamnatin yanzu ba ta da niyyar tabbatar da ɗorewar  zaman lafiyar siyasa jihar, daidaito na cikin gida da jure ra’ayoyi,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta zargi gwamnatin da yunƙurin warewa da wulaƙanta magoya bayan Jagoranta na ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda ta ce ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar gwamnatin mai ci. Ta jaddada cewa an zaɓi mataimakin gwamnan ne tare da gwamna a kan tikitin haɗin gwuiwa, don haka ba za a iya tilasta masa barin ofis bisa son rai na wasu mutane a cikin gwamnati ba.

Kwankwasiyya ta kuma ce idan gwamnatin na da wata fahimta ta adalcin siyasa, ya dace ta waiwayi abubuwan da suka faru a zaɓukan 2019 da 2023, inda Jagora Kwankwaso da miliyoyin magoya bayansa suka yi gagarumar sadaukarwa wajen samun nasarar da ta kai Gwamna Abba Kabir Yusuf da Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo zuwa Gidan Gwamnati. Ta ƙara da cewa ba za ta yi shiru ba a kan abin da ta kira cin amanar magoya baya, da tsoratarwa da wulakanta mambobinta masu biyayya.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

kwankwasiyya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

Juyin Mulki: Jami’an Sojoji 16 Za Su Fuskanci Hukuncin Kisa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.